< Zabura 88 >

1 Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
Oh Señor, Dios de mi salvación, te pido auxilio día y noche.
2 Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
Permite que mi oración venga delante de ti; escucha mi clamor.
3 Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol h7585)
Porque mi alma está llena de males, y mi vida se ha acercado al inframundo. (Sheol h7585)
4 An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
Soy contado entre los que descienden al sepulcro; Me he vuelto como un hombre sin fuerzas:
5 An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
Mi alma está entre los muertos, como en el infierno, a la que no le das más vueltas; porque están separados de tu cuidado. (questioned)
6 Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
Me has puesto en las profundidades más bajas, incluso en lugares oscuros.
7 Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
El peso de tu ira me aplasta, todas tus olas me han vencido. (Selah)
8 Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
Has enviado a mis amigos lejos de mí; me has hecho una cosa repugnante en sus ojos: estoy encerrado y no puedo salir.
9 idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
Mis ojos se están consumiendo a causa de mi problema: Señor, mi llanto ha subido a ti todos los días, mis manos están extendidas hacia ti.
10 Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
¿Harás obras de maravilla por los muertos? volverán los muertos para darte el elogio? (Selah)
11 Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
¿Se dará la historia de tu misericordia en la casa de los muertos? ¿Las noticias de tu fe llegarán al lugar de la destrucción?
12 An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
¿Puede haber conocimiento de tus maravillas en la oscuridad? o de tu justicia en la tierra del olvido?
13 Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
Pero a ti envié mi clamor, oh Señor; por la mañana mi oración vino ante ti.
14 Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
Señor, ¿por qué desechas mi alma? ¿Por qué escondes de mí tu cara?
15 Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
He estado angustiado y temeroso de la muerte desde que era joven; tu ira es dura conmigo, y no tengo fuerzas.
16 Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
El ardor de tu ira me ha sobrepasado; Estoy roto, me ha vencido.
17 Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
Me rodean todo el día como agua; han hecho un círculo sobre mí.
18 Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.
Has enviado a mis amigos y al compañero lejos de mí; Me he ido de la memoria de aquellos que son queridos por mí.

< Zabura 88 >