< Zabura 85 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ka nuna wa ƙasarka alheri, ya Ubangiji; ka mai da nasarorin Yaƙub.
For the music director. A psalm of the descendants of Korah Lord, you have shown your kindness to your land; you have restored Jacob's prosperity.
2 Ka gafarta laifin mutanenka ka kuma shafe dukan zunubansu. (Sela)
You took away your people's guilt; you forgave all their sins. (Selah)
3 Ka kau da dukan fushinka ka kuma juye daga hasalar fushinka.
You took back your fury; you turned away from your fierce anger.
4 Ka sāke mai da mu, ya Allah Mai Cetonmu, ka kau da rashin jin daɗinka daga gare mu.
Bring us back to you, God of our salvation! Take away your anger towards us.
5 Za ka ci gaba da fushi da mu har abada ne? Za ka ja fushinka cikin dukan tsararraki?
Are you going to be furious with us forever? Will you stay angry with us for all future generations?
6 Ba za ka sāke raya mu ba, don mutanenka su yi farin ciki a cikinka?
Won't you restore our lives so your people can find happiness in you?
7 Ka nuna mana ƙaunarka marar ƙarewa, ya Ubangiji, ka kuma ba mu cetonka.
Show us your trustworthy love, Lord! Give us your salvation!
8 Zan saurari abin da Allah Ubangiji zai faɗa; ya yi alkawarin salama ga mutanensa, tsarkakansa, amma kada su koma ga wauta.
Let me hear what God has to say. God speaks peace to his people, to those who trust in him. But they must not return to their foolish ways.
9 Tabbatacce cetonsa yana kusa da waɗanda suke tsoronsa, don ɗaukakarsa ta zauna a cikin ƙasarmu.
Truly God's salvation is with those who do as he says. His glorious presence will live with us in our land.
10 Ƙauna da aminci za su sadu; adalci da salama za su yi wa juna sumba.
Trustworthiness and faithful love join together; goodness and peace have kissed each other.
11 Aminci zai ɓulɓulo daga ƙasa, adalci kuma yă duba daga sama.
What is true grows up from the earth; what is right looks down from heaven.
12 Ubangiji tabbatacce zai bayar da abin da yake da kyau, ƙasarmu kuwa za tă ba da amfaninta.
The Lord will certainly give us all that is good, and our land will produce fine crops.
13 Adalci na tafiya a gabansa yana shirya hanya domin ƙafafunsa.
Truth and right go ahead of him to prepare a path for him to walk on.

< Zabura 85 >