< Zabura 84 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Na’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ina misalin kyan wurin zamanka, Ya Ubangiji Maɗaukaki!
För sångmästaren, till Gittít; av Koras söner; en psalm. Huru ljuvliga äro icke dina boningar, HERRE Sebaot!
2 Raina yana marmari, har yana suma, don filayen gidan Ubangiji; zuciyata da namana na tā da murya domin Allah mai rai.
Min själ längtar och trängtar efter HERRENS gårdar, min själ och min kropp jubla mot levande Gud.
3 Har tsada ma ta sami gida, tsatsewa kuma ta yi wa kanta sheƙa, inda za tă ƙyanƙyashe’ya’yanta, wuri kusa da bagadenka, Ya Ubangiji Maɗaukaki, Sarkina da kuma Allahna.
Ty sparven har funnit ett hus och svalan ett bo åt sig, där hon kan lägga sina ungar: dina altaren, HERRE Sebaot, min konung och min Gud.
4 Masu albarka ne waɗanda suke zama a gidanka; kullum suna ta yabonka. (Sela)
Saliga äro de som bo i ditt hus; de lova dig beständigt. (Sela)
5 Masu albarka ne waɗanda ƙarfinsu yana daga gare ka, waɗanda suka kafa zukatansu a yin tafiya zuwa wuri mai tsarki ne.
Saliga äro de människor som i dig hava sin starkhet, de vilkas håg står till dina vägar.
6 Yayinda suke wuce ta Kwarin Baka, sukan mai da shi wurin maɓulɓulai; ruwan sama na farko kuma kan rufe shi da tafkuna.
När de vandra genom Tåredalen, göra de den rik på källor, och höstregnet höljer den med välsignelser.
7 Suna ta ƙara ƙarfi, har sai kowanne ya bayyana a gaban Allah a Sihiyona.
De gå från kraft till kraft; så träda de fram inför Gud på Sion.
8 Ka ji addu’ata, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka saurare ni, ya Allah na Yaƙub. (Sela)
HERRE Gud Sebaot, hör min bön, lyssna, du Jakobs Gud. (Sela)
9 Ka dubi garkuwarmu, ya Allah; ka duba da alheri a kan shafaffenka.
Gud, vår sköld, ser härtill, och akta på din smordes ansikte.
10 Rana guda a filayen gidan sun fi dubu a wani wuri dabam; zan gwammaci in zama mai tsaron ƙofa a gidan Allahna da in zauna a tentunan mugaye.
Ty en dag i dina gårdar är bättre än eljest tusen. Jag vill hellre vakta dörren i min Guds hus än dväljas i de ogudaktigas hyddor.
11 Gama Ubangiji Allah rana ne da kuma garkuwa; Ubangiji yakan yi alheri da kuma daraja; ba ya hana kowane abu mai kyau wa waɗanda suke aikata abin da yake daidai.
Ty HERREN Gud är sol och sköld; HERREN giver nåd och ära; han vägrar icke dem något gott, som vandra i ostrafflighet.
12 Ya Ubangiji Maɗaukaki, mai albarka ne mutumin da ya dogara gare ka.
HERRE Sebaot, salig är den människa som förtröstar på dig.