< Zabura 83 >
1 Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
O God, keep thou not silence. Hold not thy peace, and be not still, O God.
2 Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
For, lo, thine enemies make a tumult, and those who hate thee have lifted up the head.
3 Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
They take crafty counsel against thy people, and consult together against thy hidden ones.
4 Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
They have said, Come, and let us cut them off from being a nation, that the name of Israel may be no more in remembrance.
5 Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
For they have consulted together with one consent. They make a covenant against thee:
6 tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
the tents of Edom, and the Ishmaelites, Moab, and the Hagarenes,
7 Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
Gebal, and Ammon, and Amalek, Philistia with the inhabitants of Tyre,
8 Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
Assyria also is joined with them; they have helped the sons of Lot. (Selah)
9 Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
Do thou to them as to Midian, as to Sisera, as to Jabin, at the river Kishon,
10 waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
who perished at Endor, who became as dung for the earth.
11 Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
Make their ranking men like Oreb and Zeeb, yea, all their rulers like Zebah and Zalmunna,
12 waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
who said, Let us take to ourselves in possession the habitations of God.
13 Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
O my God, make them like the whirling dust, as stubble before the wind,
14 kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
as the fire that burns the forest, and as the flame that sets the mountains on fire.
15 haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
So pursue them with thy tempest, and terrify them with thy storm.
16 Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
Fill their faces with confusion, that they may seek thy name, O Jehovah.
17 Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
Let them be put to shame and dismayed forever. Yea, let them be confounded and perish,
18 Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.
that they may know that thou alone, whose name is Jehovah, are the Most High over all the earth.