< Zabura 82 >

1 Zabura ta Asaf. Allah yana shugabanta cikin babban taro; yakan zartar da hukunci a cikin “alloli”.
Dios está en la reunión de Dios; él está juzgando entre los dioses.
2 “Har yaushe za ku kāre marasa adalci ku kuma goyi bayan mugaye? (Sela)
¿Hasta cuándo vas a juzgar falsamente, teniendo respeto por las personas de los malhechores? (Selah)
3 Ku tsare mutuncin marasa ƙarfi da marayu; ku kāre hakkin matalauta da waɗanda ake danniya.
Defiende la causa de los pobres y los hijos sin padres; deja que aquellos que están atribulados y en necesidad tengan sus derechos.
4 Ku ceci marasa ƙarfi da masu bukata; ku kuɓutar da su daga hannun mugaye.
Sé el salvador de los pobres y de los que no tienen nada: librarlos de la mano de los malhechores.
5 “Ba su san kome ba, ba su fahimci kome ba. Suna yawo cikin duhu; an girgiza dukan tussan duniya.
Ellos no tienen conocimiento o sentido; van en la oscuridad: todas las bases de la tierra se mueven.
6 “Na ce, ‘Ku “alloli” ne; dukanku’ya’yan Mafi Ɗaukaka’ ne.
Dije: Ustedes son dioses; todos ustedes son los hijos del Altísimo:
7 Amma za ku mutu kamar mutum kurum; za ku fāɗi kamar duk wani mai mulki.”
Pero morirás como hombres, y caerás como cualquier gobernante de la tierra.
8 Ka tashi, ya Allah, ka shari’anta duniya, gama dukan al’ummai gādonka ne.
Levántate! Oh Dios, ven como juez de la tierra; porque todas las naciones son tu herencia.

< Zabura 82 >