< Zabura 81 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga gittit. Ta Asaf. Ku rera don farin ciki ga Allah ƙarfinmu; ku yi sowa ga Allah na Yaƙub!
Au chef des chantres. Sur la Ghitit. D’Assaph. Célébrez Dieu, notre force, acclamez le Dieu de Jacob!
2 Ku fara kaɗe-kaɗe, ku buga ganga, ku kaɗa garaya da molo masu daɗi.
Chantez des hymnes, faites retentir le tambourin, la harpe suave ainsi que le luth,
3 Ku busa ƙahon rago a Sabon Wata, da kuma sa’ad da wata ya kai tsakiya, a ranar Bikinmu;
sonnez le Chofar à la nouvelle lune, au jour fixé pour notre solennité.
4 wannan ƙa’ida ce domin Isra’ila, farilla ta Allah na Yaƙub.
Car c’est une loi en Israël, une coutume en l’honneur du Dieu de Jacob;
5 Ya kafa shi a matsayin ƙa’ida domin Yusuf sa’ad da ya fito daga Masar. Muka ji yaren da ba mu fahimta ba.
c’est un témoignage qu’il établit dans Joseph, quand il marcha contre l’Egypte. J’Entendis alors des accents inconnus pour moi…
6 Ya ce, “Na kau da nauyi daga kafaɗunku; an’yantar da hannuwansu daga kwando.
J’Ai déchargé du fardeau son épaule, ses mains sont affranchies du lourd panier.
7 Cikin damuwarku kun yi kira na kuwa kuɓutar da ku, na amsa muku daga girgijen tsawa; na gwada ku a ruwan Meriba. (Sela)
Dans la détresse tu as appelé, et je t’ai délivré, je t’ai exaucé du sein mystérieux de la foudre, je t’ai éprouvé auprès des eaux de Meriba. (Sélah)
8 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa gargaɗe ku, in ba za ku saurare ni ba, ya Isra’ila!
"Ecoute, mon peuple, je veux t’adjurer; ô Israël, puisses-tu m’écouter!
9 Kada ku kasance da baƙon allah a cikinku; ba za ku rusuna ga baƙon allah ba.
Qu’il n’y ait pas chez toi de divinité étrangère, ne te prosterne pas devant un dieu du dehors.
10 Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fitar da ku daga Masar. Ku buɗe bakinku zan kuwa cika shi.
Je suis, moi, l’Eternel, ton Dieu qui t’ai tiré du pays d’Egypte. Ouvre largement ta bouche et je la remplirai."
11 “Amma mutanena ba su saurare ni ba; Isra’ila bai miƙa kansa gare ni ba.
Mais mon peuple n’a pas écouté ma voix, Israël a refusé de m’obéir.
12 Saboda haka na ba da su ga zukatansu da suka taurare don su bi dabararsu.
Je les ai donc abandonnés à l’entraînement de leur cœur, ils suivirent leurs propres inspirations.
13 “A ce mutanena za su saurare ni, a ce Isra’ila zai bi hanyoyina,
Ah! si mon peuple voulait m’écouter, Israël marcher dans mes voies,
14 da nan da nan sai in rinjayi abokan gābansu in kuma juye hannuna a kan maƙiyansu!
bien vite, je dompterais leurs ennemis, je ferais peser ma main sur leurs adversaires.
15 Waɗanda suke ƙin Ubangiji za su fāɗi a gabansa da rawar jiki, hukuncinsu kuma zai dawwama har abada.
Ceux qui haïssent l’Eternel ramperaient devant lui, mais leur bonheur, à eux, durerait toujours.
16 Amma za a ciyar da ku da alkama mafi kyau; da zuma daga dutsen da zai ƙosar da ku.”
Il les nourrirait de la mœlle du froment, et les rassasierait avec le miel des rochers.