< Zabura 80 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Lilin Alkawari.” Na Asaf. Zabura ce. Ka ji mu, ya Makiyayin Isra’ila, kai da ka bishe Yusuf kamar garke. Kai da kake zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, ka haskaka
Müzik şefi için - “Zambaklar Antlaşması” makamında - Asaf'ın mezmuru Kulak ver, ey İsrail'in çobanı, Ey Yusuf'u bir sürü gibi güden, Keruvlar arasında taht kuran, Saç ışığını,
2 a gaban Efraim, Benyamin da Manasse. Ka tā da ƙarfinka; ka zo ka cece mu.
Efrayim, Benyamin, Manaşşe önünde Uyandır gücünü, Gel, kurtar bizi!
3 Ka mai da mu, ya Allah; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
Bizi eski halimize kavuştur, ey Tanrı, Yüzünün ışığıyla aydınlat, kurtulalım!
4 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, har yaushe fushinka zai yi ta ƙuna a kan addu’o’in mutanenka?
Ya RAB, Her Şeye Egemen Tanrı, Ne zamana dek halkının dualarına ateş püsküreceksin?
5 Ka ciyar da su da burodin hawaye; ka sa suka sha hawaye ta cikakken kwaf.
Onlara ekmek yerine gözyaşı verdin, Ölçekler dolusu gözyaşı içirdin.
6 Ka mai da mu abin faɗa ga maƙwabtanmu, kuma abokan gābanmu suna mana ba’a.
Kavga nedeni ettin bizi komşularımıza, Düşmanlarımız alay ediyor bizimle.
7 Ka mai da mu, ya Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu za mu kuwa cetu.
Bizi eski halimize kavuştur, Ey Her Şeye Egemen Tanrı, Yüzünün ışığıyla aydınlat, kurtulalım!
8 Ka fitar da inabi daga Masar; ka kori al’ummai ka kuma dasa shi.
Mısır'dan bir asma çubuğu getirdin, Ulusları kovup onu diktin.
9 Ka gyara wuri saboda shi, ya kuwa yi saiwa ya cike ƙasa.
Onun için toprağı hazırladın, Kök saldı, bütün ülkeye yayıldı.
10 Aka rufe duwatsu da inuwarsa, manya-manyan itatuwan al’ul da rassansa.
Gölgesi dağları, Dalları koca sedir ağaçlarını kapladı.
11 Ya miƙe rassansa zuwa Teku tohonsa har zuwa Kogi.
Sürgünleri Akdeniz'e, Filizleri Fırat'a dek uzandı.
12 Me ya sa ka rurrushe bangayensa don duk masu wucewa su tsinke’ya’yan inabinsa?
Niçin yıktın bağın duvarlarını? Yoldan geçen herkes üzümünü koparıyor,
13 Aladu daga kurmi suna ɓarnatar da shi halittun gonaki kuma suna cinsa.
Orman domuzları onu yoluyor, Yabanıl hayvanlar onunla besleniyor.
14 Ka komo wurinmu, ya Allah Maɗaukaki! Ka duba daga sama ka gani! Ka lura da wannan inabi,
Ey Her Şeye Egemen Tanrı, ne olur, dön bize! Göklerden bak ve gör, İlgilen bu asmayla.
15 saiwar da hannun damarka ya dasa, ɗan da ka renar wa kanka.
İlgilen sağ elinin diktiği filizle, Kendine seçtiğin oğulla!
16 An yanke inabinka, an ƙone shi da wuta; a tsawatawarka mutanenka sun hallaka.
Asman kesilmiş, yakılmış, Öfkeli bakışların yok etsin düşmanlarını!
17 Bari hannunka yă zauna a kan mutumin da yake hannun damarka, ɗan mutum da ka renar wa kanka.
Elin, sağ kolun olan adamın üzerinde, Kendine seçtiğin insanın üzerinde olsun!
18 Ta haka ba za mu juye mu bar ka ba; ka rayar da mu, za mu kuwa kira bisa sunanka.
O zaman senden asla ayrılmayacağız; Yaşam ver bize, adını analım!
19 Ka mai da mu, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
Ya RAB, ey Her Şeye Egemen Tanrı, Bizi eski halimize kavuştur, Yüzünün ışığıyla aydınlat, kurtulalım!

< Zabura 80 >