< Zabura 80 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Lilin Alkawari.” Na Asaf. Zabura ce. Ka ji mu, ya Makiyayin Isra’ila, kai da ka bishe Yusuf kamar garke. Kai da kake zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, ka haskaka
In finem, pro iis qui commutabuntur. Testimonium Asaph, psalmus. Qui regis Israël, intende; qui deducis velut ovem Joseph. Qui sedes super cherubim, manifestare
2 a gaban Efraim, Benyamin da Manasse. Ka tā da ƙarfinka; ka zo ka cece mu.
coram Ephraim, Benjamin, et Manasse. Excita potentiam tuam, et veni, ut salvos facias nos.
3 Ka mai da mu, ya Allah; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
Deus, converte nos, et ostende faciem tuam, et salvi erimus.
4 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, har yaushe fushinka zai yi ta ƙuna a kan addu’o’in mutanenka?
Domine Deus virtutum, quousque irasceris super orationem servi tui?
5 Ka ciyar da su da burodin hawaye; ka sa suka sha hawaye ta cikakken kwaf.
cibabis nos pane lacrimarum, et potum dabis nobis in lacrimis in mensura?
6 Ka mai da mu abin faɗa ga maƙwabtanmu, kuma abokan gābanmu suna mana ba’a.
Posuisti nos in contradictionem vicinis nostris, et inimici nostri subsannaverunt nos.
7 Ka mai da mu, ya Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu za mu kuwa cetu.
Deus virtutum, converte nos, et ostende faciem tuam, et salvi erimus.
8 Ka fitar da inabi daga Masar; ka kori al’ummai ka kuma dasa shi.
Vineam de Ægypto transtulisti: ejecisti gentes, et plantasti eam.
9 Ka gyara wuri saboda shi, ya kuwa yi saiwa ya cike ƙasa.
Dux itineris fuisti in conspectu ejus; plantasti radices ejus, et implevit terram.
10 Aka rufe duwatsu da inuwarsa, manya-manyan itatuwan al’ul da rassansa.
Operuit montes umbra ejus, et arbusta ejus cedros Dei.
11 Ya miƙe rassansa zuwa Teku tohonsa har zuwa Kogi.
Extendit palmites suos usque ad mare, et usque ad flumen propagines ejus.
12 Me ya sa ka rurrushe bangayensa don duk masu wucewa su tsinke’ya’yan inabinsa?
Ut quid destruxisti maceriam ejus, et vindemiant eam omnes qui prætergrediuntur viam?
13 Aladu daga kurmi suna ɓarnatar da shi halittun gonaki kuma suna cinsa.
Exterminavit eam aper de silva, et singularis ferus depastus est eam.
14 Ka komo wurinmu, ya Allah Maɗaukaki! Ka duba daga sama ka gani! Ka lura da wannan inabi,
Deus virtutum, convertere, respice de cælo, et vide, et visita vineam istam:
15 saiwar da hannun damarka ya dasa, ɗan da ka renar wa kanka.
et perfice eam quam plantavit dextera tua, et super filium hominis quem confirmasti tibi.
16 An yanke inabinka, an ƙone shi da wuta; a tsawatawarka mutanenka sun hallaka.
Incensa igni et suffossa, ab increpatione vultus tui peribunt.
17 Bari hannunka yă zauna a kan mutumin da yake hannun damarka, ɗan mutum da ka renar wa kanka.
Fiat manus tua super virum dexteræ tuæ, et super filium hominis quem confirmasti tibi.
18 Ta haka ba za mu juye mu bar ka ba; ka rayar da mu, za mu kuwa kira bisa sunanka.
Et non discedimus a te: vivificabis nos, et nomen tuum invocabimus.
19 Ka mai da mu, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki; ka sa fuskarka ta haskaka a kanmu, za mu kuwa cetu.
Domine Deus virtutum, converte nos, et ostende faciem tuam, et salvi erimus.

< Zabura 80 >