< Zabura 78 >

1 Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
Eine Unterweisung Assaphs. Höre, mein Volk, mein Gesetz; neiget eure Ohren zu der Rede meines Mundes!
2 Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
Ich will meinen Mund auftun zu Sprüchen und alte Geschichte aussprechen,
3 abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
die wir gehöret haben und wissen und unsere Väter uns erzählet haben,
4 Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
daß wir's nicht verhalten sollen ihren Kindern, die hernach kommen, und verkündigen den Ruhm des HERRN und seine Macht und Wunder, die er getan hat.
5 Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
Er richtete ein Zeugnis auf in Jakob und gab ein Gesetz in Israel, das er unsern Vätern gebot, zu lehren ihre Kinder,
6 don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
auf daß die Nachkommen lerneten und die Kinder, die noch sollten geboren werden, wenn sie aufkämen, daß sie es auch ihren Kindern verkündigten,
7 Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
daß sie setzten auf Gott ihre Hoffnung und nicht vergäßen der Taten Gottes und seine Gebote hielten,
8 Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
und nicht würden wie ihre Väter, eine abtrünnige und ungehorsame Art, welchen ihr Herz nicht fest war, und ihr Geist nicht treulich hielt an Gott;
9 Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
wie die Kinder Ephraim, so geharnischt den Bogen führeten, abfielen zur Zeit des Streits.
10 ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
Sie hielten den Bund Gottes nicht und wollten nicht in seinem Gesetz wandeln,
11 Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
und vergaßen seiner Taten und seiner Wunder, die er ihnen erzeiget hatte.
12 Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
Vor ihren Vätern tat er Wunder in Ägyptenland, im Felde Zoan.
13 Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
Er zerteilete das Meer und ließ sie durchhin gehen; und stellete das Wasser wie eine Mauer.
14 Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
Er leitete sie des Tages mit einer Wolke und des Nachts mit einem hellen Feuer.
15 Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
Er riß die Felsen in der Wüste und tränkete sie mit Wasser die Fülle;
16 ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
und ließ Bäche aus dem Felsen fließen, daß sie hinabflossen wie Wasserströme.
17 Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
Noch sündigten sie weiter wider ihn und erzürneten den höchsten in der Wüste;
18 Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
und versuchten Gott in ihrem Herzen, daß sie Speise forderten für ihre Seelen;
19 Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
und redeten wider Gott und sprachen: Ja, Gott sollte wohl können einen Tisch bereiten in der Wüste!
20 Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
Siehe, er hat wohl den Felsen geschlagen, daß Wasser flossen und Bäche sich ergossen; aber wie kann er Brot geben und seinem Volk Fleisch verschaffen?
21 Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
Da nun das der HERR hörete, entbrannte er, und Feuer ging an in Jakob und Zorn kam über Israel,
22 gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
daß sie nicht glaubeten an Gott und hoffeten nicht auf seine Hilfe.
23 Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
Und er gebot den Wolken droben und tat auf die Türen des Himmels;
24 ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
und ließ das Man auf sie regnen, zu essen, und gab ihnen Himmelbrot.
25 Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
Sie aßen Engelbrot; er sandte ihnen Speise die Fülle.
26 Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
Er ließ weben den Ostwind unter dem Himmel und erregte durch seine Stärke den Südwind.
27 Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
Und ließ Fleisch auf sie regnen wie Staub und Vögel wie Sand am Meer;
28 Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
und ließ sie fallen unter ihr Lager allenthalben, da sie wohneten.
29 Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
Da aßen sie und wurden allzu satt; er ließ sie ihre Lust büßen.
30 Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
Da sie nun ihre Lust gebüßet hatten und sie noch davon aßen,
31 fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
da kam der Zorn Gottes über sie und erwürgete die Vornehmsten unter ihnen und schlug danieder die Besten in Israel.
32 Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
Aber über das alles sündigten sie noch mehr und glaubten nicht an seine Wunder.
33 Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
Darum ließ er sie dahinsterben, daß sie nichts erlangeten, und mußten ihr Leben lang geplaget sein.
34 A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
Wenn er sie erwürgete, suchten sie ihn und kehreten sich frühe zu Gott
35 Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
und gedachten, daß Gott ihr Hort ist und Gott der Höchste ihr Erlöser ist,
36 Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
und heuchelten ihm mit ihrem Munde und logen ihm mit ihrer Zunge.
37 zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
Aber ihr Herz war nicht fest an ihm und hielten nicht treulich an seinem Bunde.
38 Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
Er aber war barmherzig und vergab die Missetat und vertilgte sie nicht; und wendete oft seinen Zorn ab und ließ nicht seinen ganzen Zorn gehen.
39 Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
Denn er gedachte, daß sie Fleisch sind, ein Wind, der dahinfähret und nicht wiederkommt.
40 Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
Sie erzürneten ihn gar oft in der Wüste und entrüsteten ihn in der Einöde.
41 Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
Sie versuchten Gott immer wieder und meisterten den Heiligen in Israel.
42 Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
Sie dachten nicht an seine Hand des Tages, da er sie erlösete von den Feinden,
43 ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
wie er denn seine Zeichen in Ägypten getan hatte und seine Wunder im Lande Zoan,
44 Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
da er ihr Wasser in Blut wandelte, daß sie ihre Bäche nicht trinken konnten;
45 Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
da er Ungeziefer unter sie schickte, die sie fraßen, und Kröten, die sie verderbeten,
46 Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
und gab ihr Gewächs den Raupen und ihre Saat den Heuschrecken;
47 Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
da er ihre Weinstöcke mit Hagel schlug und ihre Maulbeerbäume mit Schloßen;
48 Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
da er ihr Vieh schlug mit Hagel und ihre Herden mit Strahlen;
49 Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
da er böse Engel unter sie sandte in seinem grimmigen Zorn und ließ sie toben und wüten und Leid tun;
50 Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
da er seinen Zorn ließ fortgehen und ihre Seelen vor dem Tode nicht verschonete und ließ ihr Vieh an der Pestilenz sterben;
51 Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
da er alle Erstgeburt in Ägypten schlug, die ersten Erben in den Hütten Hams.
52 Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
Und ließ sein Volk ausziehen wie Schafe und führete sie wie eine Herde in der Wüste.
53 Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
Und er leitete sie sicher, daß sie sich nicht fürchteten; aber ihre Feinde bedeckte das Meer.
54 Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
Und brachte sie in seine heilige Grenze, zu diesem Berge, den seine Rechte erworben hat.
55 Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
Und vor ihnen her die Völker und ließ ihnen das Erbe austeilen und ließ in jener Hütten die Stämme Israels wohnen.
56 Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
Aber sie versuchten und erzürneten Gott, den Höchsten, und hielten seine Zeugnisse nicht;
57 Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
und fielen zurück und verachteten alles, wie ihre Väter, und hielten nicht, gleichwie ein loser Bogen;
58 Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
und erzürneten ihn mit ihren Höhen und reizeten ihn mit ihren Götzen.
59 Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
Und da das Gott hörete, entbrannte er und verwarf Israel sehr,
60 Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
daß er Seine Wohnung zu Silo ließ fahren, die Hütte, da er unter Menschen wohnete;
61 Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
und gab ihre Macht ins Gefängnis und ihre HERRLIchkeit in die Hand des Feindes;
62 Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
und übergab sein Volk ins Schwert und entbrannte über sein Erbe.
63 Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
Ihre junge Mannschaft fraß das Feuer, und ihre Jungfrauen mußten ungefreiet bleiben.
64 aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
Ihre Priester fielen durchs Schwert, und waren keine Witwen, die da weinen sollten.
65 Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
Und der HERR erwachte wie ein Schlafender, wie ein Starker jauchzet, der vom Wein kommt,
66 Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
und schlug seine Feinde von hinten und hängete ihnen eine ewige Schande an.
67 Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
Und verwarf die Hütte Josephs und erwählte nicht den Stamm Ephraim,
68 amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
sondern erwählete den Stamm Juda, den Berg Zion, welchen er liebte.
69 Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
Und bauete sein Heiligtum hoch, wie ein Land, das ewiglich fest stehen soll.
70 Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
Und erwählete seinen Knecht David und nahm ihn von den Schafställen;
71 daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
von den säugenden Schafen holte er ihn, daß er sein Volk Jakob weiden sollte und sein Erbe Israel.
72 Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.
Und er weidete sie auch mit aller Treue und regierte sie mit allem Fleiß.

< Zabura 78 >