< Zabura 77 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Na Asaf. Zabura ce. Na yi kuka ga Allah don taimako; na yi kuka ga Allah don yă ji ni.
TO THE OVERSEER. FOR JEDUTHUN. A PSALM OF ASAPH. My voice [is] to God, and I cry, My voice [is] to God, And He has given ear to me.
2 Sa’ad da nake cikin damuwa, na nemi Ubangiji; da dare na miƙa hannuwa ba gajiya raina kuma ya ƙi yă ta’azantu.
I sought the Lord in a day of my distress, My hand has been spread out by night, And it does not cease, My soul has refused to be comforted.
3 Na tuna da kai, ya Allah, na kuma yi nishi; na yi nishi, ƙarfina kuwa duk ya raunana. (Sela)
I remember God, and make a noise, I meditate, and my spirit is feeble. (Selah)
4 ka hana idanuna rufewa; na damu ƙwarai har ba na iya magana.
You have taken hold of the watches of my eyes, I have been moved, and I do not speak.
5 Na yi tunani kwanakin da suka wuce, shekarun da suka wuce da daɗewa;
I have reckoned the days of old, The years of the ages.
6 na tuna da waƙoƙina da dare. Zuciyata ta yi nishi, ƙarfina kuwa ya nemi yă sani.
I remember my music in the night, I meditate with my heart, and my spirit searches diligently:
7 “Ubangiji zai ƙi ne har abada? Ba zai taɓa nuna alherinsa kuma ba?
Does the Lord cast off for all ages? Does He add to be pleased no longer?
8 Ƙaunarsa marar ƙarewa ta ɓace ke nan har abada? Alkawarinsa ya kāsa ke nan a dukan lokaci?
Has His kindness ceased forever? The saying failed from generation to generation?
9 Allah ya manta yă yi jinƙai? Cikin fushinsa ya janye tausayinsa ne?” (Sela)
Has God forgotten [His] favors? Has He shut up His mercies in anger? (Selah)
10 Sai na yi tunani, “Zan yi roƙo saboda wannan, shekarun da Mafi Ɗaukaka ya miƙa hannunsa na dama.”
And I say: “My weakness is, The changes of the right hand of the Most High.”
11 Zan tuna da ayyukan Ubangiji; I, zan tuna mu’ujizanka na tun dā.
I mention the doings of YAH, For I remember Your wonders of old,
12 Zan yi tunani a kan dukan ayyukanka in lura da dukan manyan abubuwan da ka aikata.
And I have meditated on all Your working, And I talk concerning Your doings.
13 Hanyoyinka, ya Allah, masu tsarki ne. Wanda allah ne yake da girma kamar Allahnmu?
O God, Your way [is] in holiness, Who [is] a great god like God?
14 Kai ne Allahn da yakan aikata mu’ujizai; ka nuna ikonka a cikin mutane.
You [are] the God doing wonders. You have made Your strength known among the peoples,
15 Da hannunka mai ƙarfi ka fanshi mutanenka, zuriyar Yaƙub da Yusuf. (Sela)
You have redeemed Your people with strength, The sons of Jacob and Joseph. (Selah)
16 Ruwaye sun gan ka, ya Allah, ruwaye sun gan ka suka firgita; zurfafan gaske sun girgiza.
The waters have seen You, O God, The waters have seen You, They are afraid—also depths are troubled.
17 Gizagizai sun sauko da ruwa, sararin sama suka buga tsawa; kibiyoyinka suka yi ta kai komo da walƙiya.
Thick clouds have poured out waters, The skies have given forth a noise, Also—Your arrows go up and down.
18 Aka ji tsawanka a cikin guguwa, walƙiyarka ta haskaka duniya; duniya ta yi rawar jiki ta girgiza.
The voice of Your thunder [is] in the spheres, Lightnings have lightened the world, The earth has trembled, indeed, it shakes.
19 Hanyarka ta bi ta cikin teku, hanyarka ta bi cikin manyan ruwaye, duk da haka ba a ga sawunka ba.
Your way [is] in the sea, And Your paths in many waters, And Your tracks have not been known.
20 Ka bi da mutanenka kamar garke ta hannun Musa da Haruna.
You have led Your people as a flock, By the hand of Moses and Aaron!

< Zabura 77 >