< Zabura 75 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Mai muryar “Kada A Hallaka.” Zabura ta Asaf. Waƙa ce. Muna maka godiya, ya Allah, muna maka godiya, gama Sunanka yana kusa; mutane na faɗin ayyukanka masu banmamaki.
in finem ne corrumpas psalmus Asaph cantici confitebimur tibi Deus confitebimur et invocabimus nomen tuum narrabimus mirabilia tua
2 Ka ce, “Na zaɓi ƙayyadadden lokaci; ni ne wanda yake shari’ar gaskiya.
cum accepero tempus ego iustitias iudicabo
3 Sa’ad da duniya da dukan mutanenta suka girgiza, ni ne wanda na riƙe ginshiƙan daram. (Sela)
liquefacta est terra et omnes qui habitant in ea ego confirmavi columnas eius diapsalma
4 Ga masu girman kai na ce, ‘Kada ku ƙara taƙama,’ ga mugaye kuma, ‘Kada ku ɗaga ƙahoninku.
dixi iniquis nolite inique facere et delinquentibus nolite exaltare cornu
5 Kada ku ɗaga ƙahoninku gāba da sama; kada ku yi magana da miƙaƙƙen wuya.’”
nolite extollere in altum cornu vestrum nolite loqui adversus Deum iniquitatem
6 Ba wani daga gabas ko yamma ko hamada da zai ɗaukaka mutum.
quia neque ab oriente neque ab occidente neque a desertis montibus
7 Amma Allah ne mai yin shari’a, yakan saukar da wannan, yă kuma tayar da wani.
quoniam Deus iudex est hunc humiliat et hunc exaltat
8 A hannun Ubangiji akwai kwaf cike da ruwan inabi mai kumfa gauraye da kayan yaji; yakan zuba shi, dukan mugayen duniya kuwa su sha shi tas.
quia calix in manu Domini vini meri plenus mixto et inclinavit ex hoc in hoc verum fex eius non est exinanita bibent omnes peccatores terrae
9 Game da ni dai, zan furta wannan har abada; zan rera yabo ga Allah na Yaƙub,
ego autem adnuntiabo in saeculum cantabo Deo Iacob
10 wanda ya ce, “Zan yanke ƙahonin dukan mugaye, amma za a ɗaga ƙahonin adalai sama.”
et omnia cornua peccatorum confringam et exaltabuntur cornua iusti