< Zabura 74 >

1 Maskil na Asaf. Me ya sa ka ƙi mu har abada, ya Allah? Me ya sa fushinka yake a kan tumakin kiwonka?
Un Psaume de méditation d'Asaph. Pourquoi, mon Dieu, m'as-tu repoussé pour toujours? Pourquoi ta colère est-elle excitée contre les brebis de tes pâturages?
2 Ka tuna da mutanen da ka saya tun da daɗewa, kabilar gādonka, wadda ka fansa, Dutsen Sihiyona, inda ka zauna.
Souviens-toi du troupeau que, dès le commencement, tu as acquis; tu as racheté le rameau de ton héritage, cette montagne de Sion, où tu as dressé ton tabernacle.
3 Ka juye sawunka wajen waɗannan madawwamin kufai, dukan wannan hallakar da abokin gāba ya yi wa wuri mai tsarki.
Lève les mains pour mettre fin à leur orgueil; que de mal a fait l'ennemi en tes lieux saints!
4 Maƙiyanka sun yi ruri a inda ka sadu da mu; suka kakkafa tutotinsu a matsayin alamu.
Comme ceux qui te haïssent se sont glorifiés au milieu de tes fêtes! Ils ont posé leurs étendards, comme des signaux,
5 Sun yi kamar mutane masu wāshin gatura don yanka itatuwa a kurmi.
A la porte d'en haut, sans savoir ce qu'ils faisaient. Comme dans une forêt, avec des haches,
6 Sun ragargaje dukan sassaƙar katako da gatura da kuma gudumarsu.
Ils ont frappé les battants de cette porte au même endroit; ils l'ont brisée avec la hache et le levier.
7 Suka ƙone wurinka mai tsarki ƙurmus; suka ƙazantar da mazaunin Sunanka.
Ils ont brûlé par le feu ton sanctuaire sur la terre; ils ont souillé le tabernacle de ton nom.
8 Suna cewa a zukatansu, “Za mu murƙushe su sarai!” Suka ƙone ko’ina aka yi wa Allah sujada a ƙasar.
Ils ont dit en leur cœur, et leur race, réunie au même lieu, a dit: Allons, abolissons en cette terre les fêtes du Seigneur!
9 Ba a ba mu wata alama mai banmamaki ba; ba sauran annabawan da suka ragu, kuma babu waninmu da ya sani har yaushe wannan zai ci gaba.
Nous ne voyons plus nos signes; il n'est plus de prophètes, et l'on ne nous reconnaîtra pas.
10 Har yaushe abokan gāba za su yi mana ba’a, ya Allah? Maƙiya za su ci gaba da ɓata sunanka har abada ne?
Jusques à quand, mon Dieu, l'ennemi t'outragera-t-il? L'ennemi provoquera-t-il toujours ton nom?
11 Me ya sa ka janye hannunka, hannunka na dama? Ka fid da shi daga rigarka ka hallaka su!
Pourquoi as-tu détourné ta main, ta droite du milieu de ton sein? Est-ce pour toujours?
12 Amma kai, ya Allah, kai ne sarki tun da daɗewa; ka kawo ceto a kan duniya.
Cependant Dieu, notre roi avant les siècles, a opéré notre salut au milieu de la terre.
13 Kai ne ka raba teku ta wurin ikonka; ka farfashe kawunan dodo a cikin ruwaye.
Par ta puissance tu as dompté la mer; tu as brisé sur les eaux la tête des dragons.
14 Kai ne ka murƙushe kawunan dodon ruwa ka kuma ba da shi yă zama abinci ga halittun hamada.
Tu as brisé les têtes du dragon; tu l'as donné pour nourriture aux peuples éthiopiens.
15 Kai ne ka bubbuɗe maɓulɓulai da rafuffuka; ka busar da koguna masu ruwa.
Tu as ouvert les fontaines et les torrents; tu as desséché les fleuves d'Etham.
16 Yini naka ne, dare kuma naka ne; ka kafa rana da wata.
Le jour est à toi, la nuit est à toi, tu as préparé la lune et le soleil.
17 Kai ne ka kafa dukan iyakokin duniya; ka yi rani da damina.
Tu as fait toutes les limites de la terre; tu as fait l'été et le printemps.
18 Ka tuna da yadda abokin gāba ya yi maka ba’a, ya Ubangiji, yadda wawaye suka ɓata sunanka.
Souviens-toi de ta création; l'ennemi a outragé le Seigneur, et un peuple insensé a provoqué son nom.
19 Kada ka ba da ran kurciyarka ga namun jeji; kada ka manta har abada da rayukan mutanenka masu shan azaba.
Ne livre point aux bêtes fauves l'âme qui te loue, et n'oublie pas pour toujours l'âme de tes pauvres.
20 Ka kula da alkawarinka, domin akwai tashin hankali a kowane lungu mai duhu na ƙasar.
Considère ton alliance; car les lieux obscurs de la terre sont remplis de maisons d'iniquités.
21 Kada ka bar waɗanda ake danniya su sha kunya; bari matalauta da mabukata su yabe sunanka.
Que l'affligé, que l'humble ne soient point rejetés; le pauvre et le nécessiteux loueront ton nom.
22 Ka tashi, ya Allah, ka kāre muradinka; ka tuna yadda wawaye suka yi maka ba’a dukan yini.
Lève-toi, ô Dieu, rends tes jugements; souviens-toi des outrages que te prodigue l'insensé tout le jour.
23 Kada ka ƙyale surutan ban haushi na maƙiyanka, ihun abokan gābanka, waɗanda suke ci gaba da yi.
N'oublie point la voix de tes suppliants, et que l'orgueil de ceux qui te haïssent monte toujours jusqu'à toi.

< Zabura 74 >