< Zabura 74 >

1 Maskil na Asaf. Me ya sa ka ƙi mu har abada, ya Allah? Me ya sa fushinka yake a kan tumakin kiwonka?
AN INSTRUCTION OF ASAPH. Why, O God, have You cast off forever? Your anger smokes against the flock of Your pasture.
2 Ka tuna da mutanen da ka saya tun da daɗewa, kabilar gādonka, wadda ka fansa, Dutsen Sihiyona, inda ka zauna.
Remember Your congregation [That] You purchased of old, You redeemed the rod of Your inheritance, This Mount Zion—You dwelt in it.
3 Ka juye sawunka wajen waɗannan madawwamin kufai, dukan wannan hallakar da abokin gāba ya yi wa wuri mai tsarki.
Lift up Your steps to the continuous desolations, Everything the enemy did wickedly in the sanctuary.
4 Maƙiyanka sun yi ruri a inda ka sadu da mu; suka kakkafa tutotinsu a matsayin alamu.
Your adversaries have roared, In the midst of Your meeting-places, They have set their ensigns as ensigns.
5 Sun yi kamar mutane masu wāshin gatura don yanka itatuwa a kurmi.
He is known as one bringing in on high Against a thicket of wood—axes.
6 Sun ragargaje dukan sassaƙar katako da gatura da kuma gudumarsu.
And now they break down its engravings, Together, with axe and hatchet,
7 Suka ƙone wurinka mai tsarki ƙurmus; suka ƙazantar da mazaunin Sunanka.
They have sent Your sanctuary into fire, They defiled the Dwelling Place of Your Name to the earth,
8 Suna cewa a zukatansu, “Za mu murƙushe su sarai!” Suka ƙone ko’ina aka yi wa Allah sujada a ƙasar.
They said in their hearts, “Let us oppress them together,” They burned all the meeting-places of God in the land.
9 Ba a ba mu wata alama mai banmamaki ba; ba sauran annabawan da suka ragu, kuma babu waninmu da ya sani har yaushe wannan zai ci gaba.
We have not seen our ensigns, There is no longer a prophet, Nor with us is one knowing how long.
10 Har yaushe abokan gāba za su yi mana ba’a, ya Allah? Maƙiya za su ci gaba da ɓata sunanka har abada ne?
Until when, O God, does an adversary reproach? Does an enemy despise Your Name forever?
11 Me ya sa ka janye hannunka, hannunka na dama? Ka fid da shi daga rigarka ka hallaka su!
Why do You turn back Your hand, Even Your right hand? Remove [it] from the midst of Your bosom.
12 Amma kai, ya Allah, kai ne sarki tun da daɗewa; ka kawo ceto a kan duniya.
And God [is] my king of old, Working salvation in the midst of the earth.
13 Kai ne ka raba teku ta wurin ikonka; ka farfashe kawunan dodo a cikin ruwaye.
You have divided [the] sea by Your strength, You have shattered heads of dragons by the waters,
14 Kai ne ka murƙushe kawunan dodon ruwa ka kuma ba da shi yă zama abinci ga halittun hamada.
You have broken the heads of leviathan, You make him food for the people of desert-dwellers.
15 Kai ne ka bubbuɗe maɓulɓulai da rafuffuka; ka busar da koguna masu ruwa.
You have cleaved a fountain and a stream, You have dried up perennial flowings.
16 Yini naka ne, dare kuma naka ne; ka kafa rana da wata.
The day [is] Yours, The night [is] also Yours, You have prepared a light-giver—the sun.
17 Kai ne ka kafa dukan iyakokin duniya; ka yi rani da damina.
You have set up all the borders of earth, Summer and winter—You have formed them.
18 Ka tuna da yadda abokin gāba ya yi maka ba’a, ya Ubangiji, yadda wawaye suka ɓata sunanka.
Remember this—an enemy reproached YHWH, And a foolish people have despised Your Name.
19 Kada ka ba da ran kurciyarka ga namun jeji; kada ka manta har abada da rayukan mutanenka masu shan azaba.
Do not give up to a [wild] creature, The soul of Your turtle-dove, Do not forget the life of Your poor ones forever.
20 Ka kula da alkawarinka, domin akwai tashin hankali a kowane lungu mai duhu na ƙasar.
Look attentively to the covenant, For the dark places of earth, Have been full of habitations of violence.
21 Kada ka bar waɗanda ake danniya su sha kunya; bari matalauta da mabukata su yabe sunanka.
Do not let the oppressed turn back ashamed, Let the poor and needy praise Your Name,
22 Ka tashi, ya Allah, ka kāre muradinka; ka tuna yadda wawaye suka yi maka ba’a dukan yini.
Arise, O God, plead Your plea, Remember Your reproach from a fool all the day.
23 Kada ka ƙyale surutan ban haushi na maƙiyanka, ihun abokan gābanka, waɗanda suke ci gaba da yi.
Do not forget the voice of Your adversaries, The noise of Your withstanders is going up continually!

< Zabura 74 >