< Zabura 72 >

1 Ta Solomon. Ka tanada sarki da shari’arka ta gaskiya, ya Allah, ɗan sarki da adalcinka.
Ó Deus, dá ao rei dos teus juizos, e a tua justiça ao filho do rei.
2 Zai shari’anta mutanenka da adalci, marasa ƙarfinka da shari’ar gaskiya.
Elle julgará ao teu povo com justiça, e aos teus pobres com juizo.
3 Duwatsu za su kawo wadata ga mutane, tuddai kuma su ba da amfani na adalci.
Os montes trarão paz ao povo e os outeiros com justiça.
4 Zai kāre marasa ƙarfi a cikin mutane yă kuma cece’ya’yan masu bukata; zai murƙushe masu danniya.
Julgará os afflictos do povo, salvará os filhos do necessitado, e quebrantará o oppressor.
5 Zai jimre muddin rana tana nan, muddin akwai wata, har dukan zamanai.
Temer-te-hão emquanto durar o sol e a lua, de geração em geração.
6 Zai zama kamar ruwan sama mai fāɗuwa a filin ciyayin da aka yanka, kamar yayyafi mai ba wa duniya ruwa.
Elle descerá como a chuva sobre a herva ceifada, como os chuveiros que humedecem a terra.
7 A kwanakinsa adalai za su haɓaka wadata za tă yalwata har sai babu sauran wata.
Nos seus dias florescerá o justo, e abundancia de paz emquanto durar a lua.
8 Zai yi mulki daga teku zuwa teku kuma daga Kogi zuwa iyakar duniya.
Dominará de mar a mar, e desde o rio até ás extremidades da terra.
9 Kabilun hamada za su rusuna a gabansa abokan gābansa kuwa za su lashe ƙura.
Aquelles que habitam no deserto se inclinarão ante elle, e os seus inimigos lamberão o pó.
10 Sarakunan Tarshish da na bakin kogi masu nisa za su ba da gandu gare shi; sarakunan Sheba da Seba za su ba shi kyautai.
Os reis de Tarsis e das ilhas trarão presentes; os reis de Sheba e de Saba offerecerão dons.
11 Dukan sarakuna za su rusuna masa kuma dukan al’ummai za su bauta masa.
E todos os reis se prostrarão perante elle; todas as nações o servirão.
12 Gama zai ceci masu bukatan da suka yi kuka, marasa ƙarfin da ba su da mai taimako.
Porque elle livrará ao necessitado quando clamar, como tambem ao afflicto e ao que não tem quem o ajude.
13 Zai ji tausayin gajiyayyu da masu bukata yă ceci masu bukata daga mutuwa.
Compadecer-se-ha do pobre e do afflicto, e salvará as almas dos necessitados.
14 Zai kuɓutar da su daga danniya da rikici, gama jininsu yake a gabansa.
Libertará as suas almas do engano e da violencia, e precioso será o seu sangue aos olhos d'elle.
15 Bari yă yi doguwar rayuwa! Bari a ba shi zinariya daga Sheba. Bari mutane su riƙa yin addu’a dominsa su kuma albarkace shi dukan yini.
E viverá, e se lhe dará do oiro de Sheba; e continuamente se fará por elle oração; e todos os dias o bemdirão.
16 Bari hatsi yă yalwata a duk fāɗin ƙasar; bari yă cika bisan tuddai. Bari’ya’yan itatuwansa su haɓaka kamar Lebanon; bari yă bazu kamar ciyayi a gona.
Haverá um punhado de trigo em terra sobre as cabeças dos montes; o seu fructo se abalará como o Libano, e os da cidade florescerão como a herva da terra.
17 Bari sunansa yă dawwama har abada; bari yă ci gaba muddin rana tana nan. Dukan al’ummai za su sami albarka ta wurinsa, za su kuma ce da shi mai albarka.
O seu nome permanecerá eternamente; o seu nome se irá propagando de paes a filhos emquanto o sol durar, e os homens serão abençoados n'elle; todas as nações lhe chamarão bemaventurado.
18 Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah, Allah na Isra’ila, wanda shi kaɗai ya aikata abubuwa masu banmamaki.
Bemdito seja o Senhor Deus, o Deus d'Israel, que só elle faz maravilhas.
19 Yabo ya tabbata ga sunansa mai ɗaukaka har abada; bari dukan duniya ta cika da ɗaukakarsa.
E bemdito seja para sempre o seu nome glorioso; e encha-se toda a terra da sua gloria. Amen e Amen.
20 Wannan ya kammala addu’o’in Dawuda ɗan Yesse.
Aqui acabam as orações de David, filho de Jessé.

< Zabura 72 >