< Zabura 71 >

1 A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka taɓa sa in sha kunya.
Ya RAB, sana sığınıyorum, Utandırma beni hiçbir zaman!
2 Ka kuɓutar da ni ka cece ni cikin adalcinka; ka juya kunnenka gare ni ka kuma cece ni.
Adaletinle kurtar beni, tehlikeden uzaklaştır, Kulak ver bana, kurtar beni!
3 Ka zama dutsena da kagarata, inda kullum zan je. Ka ba da umarni a cece ni, gama kai ne dutsen ɓuyana da katangata.
Sığınacak kayam ol, Her zaman başvurabileceğim; Buyruk ver, kurtulayım, Çünkü kayam ve kalem sensin.
4 Ka cece ni, ya Allahna, daga hannun mugaye, da kuma daga ikon mugaye da masu mugunta.
Ey Tanrım, kurtar beni Kötünün elinden, haksızın, gaddarın pençesinden!
5 Gama kai ne abin sa zuciyata, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ƙarfin zuciyata tun ina yaro.
Çünkü umudum sensin, ey Egemen RAB, Gençliğimden beri dayanağım sensin.
6 Daga haihuwa na dogara gare ka; kai ka kawo ni daga cikin mahaifiyata. Kullayaumi zan yabe ka.
Doğduğum günden beri sana güveniyorum, Beni ana rahminden çıkaran sensin. Övgülerim hep sanadır.
7 Na zama kamar abin sa zuciya ga yawanci, amma kai ne katangata mai ƙarfi.
Birçokları için iyi bir örnek oldum, Çünkü sen güçlü sığınağımsın.
8 Bakina ya cika da yabonka, ina furta darajarka dukan yini.
Ağzımdan sana övgü eksilmez, Gün boyu yüceliğini anarım.
9 Kada ka yar da ni sa’ad da na tsufa; kada ka yashe ni sa’ad da ƙarfina ya ƙare.
Yaşlandığımda beni reddetme, Gücüm tükendiğinde beni terk etme!
10 Gama abokan gābana suna magana a kaina; waɗanda suke jira su kashe ni suna haɗa baki tare.
Çünkü düşmanlarım benden söz ediyor, Beni öldürmek isteyenler birbirine danışıyor,
11 Suna cewa, “Allah ya yashe shi; mu fafare shi mu kama shi, gama ba wanda zai kuɓutar da shi.”
“Tanrı onu terk etti” diyorlar, “Kovalayıp yakalayın, Kurtaracak kimsesi yok!”
12 Kada ka yi nisa da ni, ya Allah; zo da sauri, ya Allahna, ka taimake ni.
Ey Tanrı, benden uzak durma, Tanrım, yardımıma koş!
13 Bari masu zagina su hallaka da kunya; bari waɗanda suke so su cutar da ni su sha ba’a da kuma kunya.
Utansın, yok olsun beni suçlayanlar, Utanca, rezalete bürünsün kötülüğümü isteyenler.
14 Amma game da ni, kullayaumi zan kasance da sa zuciya; zan yabe ka sau da sau.
Ama ben her zaman umutluyum, Sana övgü üstüne övgü dizeceğim.
15 Bakina zai ba da labarin adalcinka, zai yi maganar cetonka dukan yini, ko da yake ban san yawansa ba.
Gün boyu senin zaferini, Kurtarışını anlatacağım, Ölçüsünü bilmesem de.
16 Zan zo in furta in kuma yi shelar ayyukanka masu girma, ya Ubangiji Mai Iko Duka; zan yi shelar adalcinka, naka kaɗai.
Ey Egemen RAB, gelip yiğitliklerini, Senin, yalnız senin zaferini duyuracağım.
17 Tun ina yaro, ya Allah, ka koya mini har wa yau ina furta ayyukanka masu banmamaki.
Ey Tanrı, çocukluğumdan beri beni sen yetiştirdin, Senin harikalarını hâlâ anlatıyorum.
18 Ko sa’ad da na tsufa da furfura, kada ka yashe ni, ya Allah, sai na furta ikonka ga tsara mai zuwa, ƙarfinka ga dukan waɗanda suke zuwa.
Yaşlanıp saçlarıma ak düşse bile Terk etme beni, ey Tanrı, Gücünü gelecek kuşağa, Kudretini sonrakilere anlatana dek.
19 Adalcinka ya kai sararin sama, ya Allah, kai da ka yi manyan abubuwa. Wane ne kamar ka, ya Allah?
Ey Tanrı, doğruluğun göklere erişiyor, Büyük işler yaptın, Senin gibisi var mı, ey Tanrı?
20 Ko da yake ka sa na ga wahaloli, masu yawa da kuma masu ɗaci, za ka sāke mayar mini da rai; daga zurfafan duniya za ka sāke tā da ni.
Sen ki, bana birçok kötü sıkıntı gösterdin, Bana yeniden yaşam verecek, Beni toprağın derinliklerinden çıkaracaksın.
21 Za ka ƙara girmana ka sāke ta’azantar da ni.
Saygınlığımı artıracak, Yine beni avutacaksın.
22 Zan yabe ka da garaya saboda amincinka, ya Allah; zan rera yabo gare ka da molo, Ya Mai Tsarki na Isra’ila.
Ben de seni, Senin sadakatini çenkle öveceğim, ey Tanrım, Lir çalarak seni ilahilerle öveceğim, Ey İsrail'in Kutsalı!
23 Leɓunana za su yi sowa don farin ciki sa’ad da na rera yabo gare ka, ni, wanda ka fansa.
Seni ilahilerle överken, Dudaklarımla, varlığımla sevincimi dile getireceğim, Çünkü sen beni kurtardın.
24 Harshena zai ba da labarin ayyukanka masu adalci dukan yini, gama waɗanda suka so su cutar da ni sun sha kunya suka kuma rikice.
Dilim gün boyu senin zaferinden söz edecek, Çünkü kötülüğümü isteyenler Utanıp rezil oldu.

< Zabura 71 >