< Zabura 7 >

1 Wani shiggayiyon ta Dawuda, wanda Ya Rera wa Ubangiji game da Kush mutumin Benyamin. Ya Ubangiji Allahna, na zo neman mafaka a wurinka; ka cece ni ka kuɓutar da ni daga dukan waɗanda suke bi na,
Lamentación que David entonó con ocasión de las palabras de Cus, hijo de Benjamín. Yahvé, Dios mío, a Ti me acojo; líbrame de todo el que me persigue, y ponme a salvo;
2 in ba haka ba za su yayyage ni kamar zaki su ɓarke ni kucu-kucu ba tare da wani da zai cece ni ba.
no sea que arrebate mi vida, como león, y me despedace, sin que haya quien me salve.
3 Ya Ubangiji Allahna, in na yi kuskure aka kuwa sami laifi a hannuwana,
Yahvé, Dios mío, si yo hice eso, si hay en mis manos iniquidad;
4 in na yi mugunta ga wanda yake zaman lafiya da ni ko kuwa ba da wani dalilin cuci abokin gābana,
si he hecho mal a mi amigo -yo, que salvé a los que me oprimían injustamente-
5 to, bari abokin gābana yă bi yă kuma cim mini; bari yă tattake raina a ƙasa ya sa in kwana a ƙura. (Sela)
persígame el enemigo y apodérese de mí; aplaste mi vida en el suelo y arrastre mi honor por el fango.
6 Ka tashi, ya Ubangiji, cikin fushinka; ka tashi gāba da fushin abokan gābana. Ka farka, Allahna, ka umarta adalci.
Despierta, Yahvé, en tu ira; yérguete contra la rabia de los que me oprimen. Levántate a mi favor en el juicio que tienes decretado
7 Bari taron mutane su taru kewaye da kai. Ka yi mulki a bisansu daga bisa;
Te rodee la congregación de los pueblos y siéntate sobre ella en lo alto.
8 bari Ubangiji mai shari’ar mutane. Ka shari’anta ni Ya Ubangiji, bisa ga adalcina, bisa ga mutuncina, ya Mafi Ɗaukaka.
Yahvé va juzgar a las naciones. Hazme a mí justicia, Yahvé, según mi rectitud, y según la inocencia que hay en mí.
9 Ya Allah mai adalci, wanda yake binciken tunani da zukata, ka kawo ƙarshen rikicin mugaye ka kuma sa adalai su zauna lafiya.
Cese ya la malicia de los impíos y confirma Tú al justo, ¡oh justo Dios, que sondeas los corazones y las entrañas!
10 Garkuwata shi ne Allah Mafi Ɗaukaka, wanda yake ceton masu tsabtar zuciya.
Mi defensa está en Dios, que salva a los rectos de corazón.
11 Allah alƙali ne mai adalci, Allahn da yakan bayyana fushinsa kowace rana.
Dios, justo Juez, fuerte y paciente, tiene pronta su ira cada día.
12 In mutum bai tuba ba, Allah zai wasa takobinsa; zai tanƙware yă kuma ɗaura bakansa.
Si no se convierte afilará su espada, entesará su arco y apuntará;
13 Ya shirya makamansa masu dafi; ya shirya kibiyoyinsa masu wuta.
tiene preparadas para ellos flechas mortales; hará de fuego sus saetas.
14 Wanda yake da cikin mugunta ya kuma ɗauki cikin damuwa yakan haifi ƙarya.
Mirad al que concibió la iniquidad: quedó grávido de malicia y dio a luz la traición.
15 Wanda ya haƙa rami yakan fāɗa cikin ramin da ya haƙa.
Cavó una fosa y la ahondó, mas cayó en el hoyo que él hizo.
16 Damuwar da ya ja yakan sāke nannaɗe a kansa; fitinarsa takan sauka a kansa.
En su propia cabeza recaerá su malicia, y sobre su cerviz descenderá su iniquidad.
17 Zan gode wa Ubangiji saboda adalcinsa zan kuma rera yabo ga sunan Ubangiji Mafi Ɗaukaka.
Mas yo alabaré a Yahvé por su justicia, y cantaré salmos al Nombre de Yahvé Altísimo.

< Zabura 7 >