< Zabura 69 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin.” Ta Dawuda. Ka cece ni, ya Allah, gama ruwa ya kai wuyata
다윗의 시, 영장으로 소산님에 맞춘 노래 하나님이여 나를 구원하소서 물들이 내 영혼까지 흘러 들어왔나이다
2 Na nutse cikin laka mai zurfi, inda babu wurin tsayawa. Na shiga cikin ruwaye masu zurfi; rigyawa ya sha kaina.
내가 설 곳이 없는 깊은 수렁에 빠지며 깊은 물에 들어가니 큰 물이 내게 넘치나이다
3 Na gaji da kira ina neman taimako; maƙogwarona ya bushe idanuna sun dushe, suna neman Allahna.
내가 부르짖음으로 피곤하여 내 목이 마르며 내 하나님을 바람으로 내 눈이 쇠하였나이다
4 Waɗanda suke ƙina ba dalili sun fi gashin kaina yawa; da yawa ne abokan gābana babu dalili, su da suke nema su hallaka ni. An tilasta mini in mayar da abin da ban sata ba.
무고히 나를 미워하는 자가 내 머리털보다 많고 무리히 내 원수가 되어 나를 끊으려 하는 자가 강하였으니 내가 취치 아니한 것도 물어 주게 되었나이다
5 Ka san wautata, ya Allah; laifina ba a ɓoye yake daga gare ka ba.
하나님이여 나의 우매함을 아시오니 내 죄가 주의 앞에서 숨김이 없나이다
6 Bari waɗanda suke sa zuciya gare ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki; bari waɗanda suke neman ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Allah na Isra’ila.
만군의 주 여호와여 주를 바라는 자로 나를 인하여 수치를 당케 마옵소서 이스라엘의 하나님이여 주를 찾는 자로 나를 인하여 욕을 당케 마옵소서
7 Gama na jimre da ba’a saboda kai, kunya kuma ta rufe fuskata.
내가 주를 위하여 훼방을 받았사오니 수치가 내 얼굴에 덮였나이다
8 Ni baƙo ne a cikin’yan’uwana, bare kuma ga’ya’yan mahaifiyata maza;
내가 내 형제에게는 객이 되고 내 모친의 자녀에게는 외인이 되었나이다
9 gama himma da nake yi wa gidanka yana ƙunata, kuma zagi na masu zaginka yana fāɗuwa a kaina.
주의 집을 위하는 열성이 나를 삼키고 주를 훼방하는 훼방이 내게 미쳤나이다
10 Sa’ad da na yi kuka na kuma yi azumi dole in jimre da ba’a;
내가 곡하고 금식함으로 내 영혼을 경계하였더니 그것이 도리어 나의 욕이 되었으며
11 sa’ad da na sanya rigunan makoki, mutane suna maishe ni abin dariya.
내가 굵은 베로 내 옷을 삼았더니 내가 저희의 말거리가 되었나이다
12 Masu zama a ƙofa suna mini ba’a, na zama waƙa a bakin bugaggu da giya.
성문에 앉은 자가 나를 말하며 취한 무리가 나를 가져 노래하나이다
13 Amma na yi addu’a gare ka, ya Ubangiji, a lokacin da ka ga dama; a cikin ƙaunarka mai girma, ya Allah, ka amsa mini da tabbacin ceto.
여호와여 열납하시는 때에 나는 주께 기도하오니 하나님이여 많은 인자와 구원의 진리로 내게 응답하소서
14 Ka fid da ni daga laka, kada ka bari in nutse; ka cece ni daga waɗanda suke ƙina, daga rurin ruwaye.
나를 수렁에서 건지사 빠지지 말게 하시고 나를 미워하는 자에게서와 깊은 물에서 건지소서
15 Kada ka bar rigyawa yă sha kaina ko zurfafa su haɗiye ni ko rami yă rufe bakinsa a kaina.
큰 물이 나를 엄몰하거나 깊음이 나를 삼키지 못하게 하시며 웅덩이로 내 위에 그 입을 닫지 못하게 하소서
16 Ka amsa mini, ya Ubangiji cikin alherin ƙaunarka; cikin jinƙanka mai girma ka juyo gare ni.
여호와여 주의 인자하심이 선하시오니 내게 응답하시며 주의 많은 긍휼을 따라 내게로 돌이키소서
17 Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka; ka amsa mini da sauri, gama ina cikin wahala.
주의 얼굴을 주의 종에게서 숨기지 마소서 내가 환난 중에 있사오니 속히 내게 응답하소서
18 Ka zo kusa ka kuɓutar da ni; ka fanshe ni saboda maƙiyana.
내 영혼에게 가까이 하사 구속하시며 내 원수를 인하여 나를 속량 하소서
19 Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya; dukan abokan gābana suna a gabanka.
주께서 나의 훼방과 수치와 능욕을 아시나이다 내 대적이 다 주의 앞에 있나이다
20 Ba’a ta sa zuciyata ta karai ta bar ni ba mataimaki; Na nemi a ji tausayina, amma ban sami ko ɗaya ba, na nemi masu ta’aziyya, amma ban sami ko ɗaya ba.
훼방이 내 마음을 상하여 근심이 충만하니 긍휼히 여길 자를 바라나 없고 안위할 자를 바라나 찾지 못하였나이다
21 Sun sa abin ɗaci cikin abincina suka kuma ba ni ruwan inabi mai tsami sa’ad da nake jin ƙishi.
저희가 쓸개를 나의 식물로 주며 갈할 때에 초로 마시웠사오니
22 Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko; bari yă zama sakamakon laifi da kuma tarko.
저희 앞에 밥상이 올무가 되게 하시며 저희 평안이 덫이 되게 하소서
23 Bari idanunsu yă dushe don kada su gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.
저희 눈이 어두워 보지 못하게 하시며 그 허리가 항상 떨리게 하소서
24 Ka kwarara fushinka a kansu; bari fushinka mai zafi yă ci musu.
주의 분노를 저희 위에 부으시며 주의 맹렬하신 노로 저희에게 미치게 하소서
25 Bari wurinsu yă zama kufai; kada ka bar wani yă zauna a tentunansu.
저희 거처로 황폐하게 하시며 그 장막에 거하는 자가 없게 하소서
26 Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta suna kuma taɗin wahalar waɗanda ka ji musu rauni.
대저 저희가 주의 치신 자를 핍박하며 주께서 상케 하신 자의 슬픔을 말하였사오니
27 Ka neme su da laifi a kan laifi; kada ka bar su su sami rabo a cikin cetonka.
저희 죄악에 죄악을 더 정하사 주의 의에 들어오지 못하게 하소서
28 Bari a shafe su sarai daga littafin rai kada a kuma lissafta su tare da adalai.
저희를 생명책에서 도말하사 의인과 함께 기록되게 마소서
29 Ina cikin zafi da kuma azaba; bari cetonka, ya Allah, yă tsare ni.
오직 나는 가난하고 슬프오니 하나님이여 주의 구원으로 나를 높이소서
30 Zan yabe sunan Allah cikin waƙa in kuma ɗaukaka shi tare wurin yin godiya.
내가 노래로 하나님의 이름을 찬송하며 감사함으로 하나님을 광대하시다 하리니
31 Wannan zai gamshi Ubangiji fiye da saniya, fiye da bijimi da ƙahoninsa da kuma kofatansa.
이것이 소 곧 뿔과 굽이 있는 황소를 드림보다 여호와를 더욱 기쁘시게 함이 될 것이라
32 Matalauta za su gani su kuma yi murna, ku da kuke neman Allah, bari zukatanku su rayu!
온유한 자가 이를 보고 기뻐하나니 하나님을 찾는 너희들아 너희 마음을 소생케 할지어다
33 Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.
여호와는 궁핍한 자를 들으시며 자기를 인하여 수금된 자를 멸시치 아니하시나니
34 Bari sama da ƙasa su yabe shi, tekuna da dukan abin da yake motsi a cikinsu,
천지가 그를 찬송할 것이요 바다와 그 중의 모든 동물도 그리할지로다
35 gama Allah zai cece Sihiyona yă sāke gina biranen Yahuda. Sa’an nan mutane za su zauna a can su mallake ta,
하나님이 시온을 구원하시고 유다 성읍들을 건설하시리니 무리가 거기 거하여 소유를 삼으리로다
36 ’ya’yan bayinsa za su gāje ta, waɗanda kuma suna ƙaunar sunansa za su zauna a can.
그 종들의 후손이 또한 이를 상속하고 그 이름을 사랑하는 자가 그 중에 거하리로다

< Zabura 69 >