< Zabura 69 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin.” Ta Dawuda. Ka cece ni, ya Allah, gama ruwa ya kai wuyata
Au chef des chantres. Sur les lis. De David. Sauve-moi, ô Dieu! Car les eaux menacent ma vie.
2 Na nutse cikin laka mai zurfi, inda babu wurin tsayawa. Na shiga cikin ruwaye masu zurfi; rigyawa ya sha kaina.
J’enfonce dans la boue, sans pouvoir me tenir; Je suis tombé dans un gouffre, et les eaux m’inondent.
3 Na gaji da kira ina neman taimako; maƙogwarona ya bushe idanuna sun dushe, suna neman Allahna.
Je m’épuise à crier, mon gosier se dessèche, Mes yeux se consument, tandis que je regarde vers mon Dieu.
4 Waɗanda suke ƙina ba dalili sun fi gashin kaina yawa; da yawa ne abokan gābana babu dalili, su da suke nema su hallaka ni. An tilasta mini in mayar da abin da ban sata ba.
Ils sont plus nombreux que les cheveux de ma tête, Ceux qui me haïssent sans cause; Ils sont puissants, ceux qui veulent me perdre, Qui sont à tort mes ennemis. Ce que je n’ai pas dérobé, il faut que je le restitue.
5 Ka san wautata, ya Allah; laifina ba a ɓoye yake daga gare ka ba.
O Dieu! Tu connais ma folie, Et mes fautes ne te sont point cachées.
6 Bari waɗanda suke sa zuciya gare ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki; bari waɗanda suke neman ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Allah na Isra’ila.
Que ceux qui espèrent en toi ne soient pas confus à cause de moi, Seigneur, Éternel des armées! Que ceux qui te cherchent ne soient pas dans la honte à cause de moi, Dieu d’Israël!
7 Gama na jimre da ba’a saboda kai, kunya kuma ta rufe fuskata.
Car c’est pour toi que je porte l’opprobre, Que la honte couvre mon visage;
8 Ni baƙo ne a cikin’yan’uwana, bare kuma ga’ya’yan mahaifiyata maza;
Je suis devenu un étranger pour mes frères, Un inconnu pour les fils de ma mère.
9 gama himma da nake yi wa gidanka yana ƙunata, kuma zagi na masu zaginka yana fāɗuwa a kaina.
Car le zèle de ta maison me dévore, Et les outrages de ceux qui t’insultent tombent sur moi.
10 Sa’ad da na yi kuka na kuma yi azumi dole in jimre da ba’a;
Je verse des larmes et je jeûne, Et c’est ce qui m’attire l’opprobre;
11 sa’ad da na sanya rigunan makoki, mutane suna maishe ni abin dariya.
Je prends un sac pour vêtement, Et je suis l’objet de leurs sarcasmes.
12 Masu zama a ƙofa suna mini ba’a, na zama waƙa a bakin bugaggu da giya.
Ceux qui sont assis à la porte parlent de moi, Et les buveurs de liqueurs fortes me mettent en chansons.
13 Amma na yi addu’a gare ka, ya Ubangiji, a lokacin da ka ga dama; a cikin ƙaunarka mai girma, ya Allah, ka amsa mini da tabbacin ceto.
Mais je t’adresse ma prière, ô Éternel! Que ce soit le temps favorable, ô Dieu, par ta grande bonté! Réponds-moi, en m’assurant ton secours!
14 Ka fid da ni daga laka, kada ka bari in nutse; ka cece ni daga waɗanda suke ƙina, daga rurin ruwaye.
Retire-moi de la boue, et que je n’enfonce plus! Que je sois délivré de mes ennemis et du gouffre!
15 Kada ka bar rigyawa yă sha kaina ko zurfafa su haɗiye ni ko rami yă rufe bakinsa a kaina.
Que les flots ne m’inondent plus, Que l’abîme ne m’engloutisse pas, Et que la fosse ne se ferme pas sur moi!
16 Ka amsa mini, ya Ubangiji cikin alherin ƙaunarka; cikin jinƙanka mai girma ka juyo gare ni.
Exauce-moi, Éternel! Car ta bonté est immense. Dans tes grandes compassions, tourne vers moi les regards,
17 Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka; ka amsa mini da sauri, gama ina cikin wahala.
Et ne cache pas ta face à ton serviteur! Puisque je suis dans la détresse, hâte-toi de m’exaucer!
18 Ka zo kusa ka kuɓutar da ni; ka fanshe ni saboda maƙiyana.
Approche-toi de mon âme, délivre-la! Sauve-moi, à cause de mes ennemis!
19 Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya; dukan abokan gābana suna a gabanka.
Tu connais mon opprobre, ma honte, mon ignominie; Tous mes adversaires sont devant toi.
20 Ba’a ta sa zuciyata ta karai ta bar ni ba mataimaki; Na nemi a ji tausayina, amma ban sami ko ɗaya ba, na nemi masu ta’aziyya, amma ban sami ko ɗaya ba.
L’opprobre me brise le cœur, et je suis malade; J’attends de la pitié, mais en vain, Des consolateurs, et je n’en trouve aucun.
21 Sun sa abin ɗaci cikin abincina suka kuma ba ni ruwan inabi mai tsami sa’ad da nake jin ƙishi.
Ils mettent du fiel dans ma nourriture, Et, pour apaiser ma soif, ils m’abreuvent de vinaigre.
22 Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko; bari yă zama sakamakon laifi da kuma tarko.
Que leur table soit pour eux un piège, Et un filet au sein de leur sécurité!
23 Bari idanunsu yă dushe don kada su gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.
Que leurs yeux s’obscurcissent et ne voient plus, Et fais continuellement chanceler leurs reins!
24 Ka kwarara fushinka a kansu; bari fushinka mai zafi yă ci musu.
Répands sur eux ta colère, Et que ton ardente fureur les atteigne!
25 Bari wurinsu yă zama kufai; kada ka bar wani yă zauna a tentunansu.
Que leur demeure soit dévastée, Qu’il n’y ait plus d’habitants dans leurs tentes!
26 Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta suna kuma taɗin wahalar waɗanda ka ji musu rauni.
Car ils persécutent celui que tu frappes, Ils racontent les souffrances de ceux que tu blesses.
27 Ka neme su da laifi a kan laifi; kada ka bar su su sami rabo a cikin cetonka.
Ajoute des iniquités à leurs iniquités, Et qu’ils n’aient point part à ta miséricorde!
28 Bari a shafe su sarai daga littafin rai kada a kuma lissafta su tare da adalai.
Qu’ils soient effacés du livre de vie, Et qu’ils ne soient point inscrits avec les justes!
29 Ina cikin zafi da kuma azaba; bari cetonka, ya Allah, yă tsare ni.
Moi, je suis malheureux et souffrant: O Dieu, que ton secours me relève!
30 Zan yabe sunan Allah cikin waƙa in kuma ɗaukaka shi tare wurin yin godiya.
Je célébrerai le nom de Dieu par des cantiques, Je l’exalterai par des louanges.
31 Wannan zai gamshi Ubangiji fiye da saniya, fiye da bijimi da ƙahoninsa da kuma kofatansa.
Cela est agréable à l’Éternel, plus qu’un taureau Avec des cornes et des sabots.
32 Matalauta za su gani su kuma yi murna, ku da kuke neman Allah, bari zukatanku su rayu!
Les malheureux le voient et se réjouissent; Vous qui cherchez Dieu, que votre cœur vive!
33 Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.
Car l’Éternel écoute les pauvres, Et il ne méprise point ses captifs.
34 Bari sama da ƙasa su yabe shi, tekuna da dukan abin da yake motsi a cikinsu,
Que les cieux et la terre le célèbrent, Les mers et tout ce qui s’y meut!
35 gama Allah zai cece Sihiyona yă sāke gina biranen Yahuda. Sa’an nan mutane za su zauna a can su mallake ta,
Car Dieu sauvera Sion, et bâtira les villes de Juda; On s’y établira, et l’on en prendra possession;
36 ’ya’yan bayinsa za su gāje ta, waɗanda kuma suna ƙaunar sunansa za su zauna a can.
La postérité de ses serviteurs en fera son héritage, Et ceux qui aiment son nom y auront leur demeure.

< Zabura 69 >