< Zabura 66 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
En Psalmvisa, till att föresjunga. Fröjdens Gudi, all land.
2 Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
Lofsjunger, till att ära hans Namn; priser honom härliga.
3 Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
Säger till Gud: Huru underliga äro dina gerningar! Dinom fiendom skall fela för dine stora magt.
4 Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
All land tillbedje dig, och lofsjunge dig; lofsjunge dino Namne. (Sela)
5 Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
Kommer och ser uppå Guds verk; den så underlig är i sina gerningar, ibland menniskors barn.
6 Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
Han förvandlar hafvet uti det torra, så att man till fot öfver vattnet går. Dess fröjde vi oss i honom.
7 Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
Han är rådandes med sine kraft evinnerliga; hans ögon skåda på folken. De affällige skola icke kunna upphäfva sig. (Sela)
8 Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
Lofver, I folk, vår Gud; låter hans lof vidt hördt varda;
9 ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
Den våra själ vid lif behåller, och låter våra fötter icke slinta.
10 Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
Ty, Gud, du hafver försökt oss, och pröfvat oss, såsom silfver pröfvadt varder.
11 Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
Du hafver fört oss uti häktelse; du hafver lagt en tunga på våra länder.
12 Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
Du hafver låtit komma menniskor öfver vårt hufvud. Vi äre komne i eld och i vatten; men du hafver utfört oss, och vederqvickt oss.
13 Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
Derföre vill jag med bränneoffer gå in uti ditt hus, och betala dig mina löften;
14 alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
Såsom jag mina läppar upplåtit hafver, och min mun talat hafver, i mine nöd.
15 Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
Jag vill göra dig fet bränneoffer af brändom vädrom; jag vill offra oxar och bockar. (Sela)
16 Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
Kommer hit, hörer till, alle I som Gud frukten; jag vill förtälja, hvad han mine själ gjort hafver.
17 Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
Till honom ropade jag med min mun, och prisade honom med mine tungo.
18 Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
Om jag något orätt förehade i mitt hjerta, så, vorde Herren mig ej hörandes.
19 amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
Derföre hörer mig Gud, och aktar uppå min bön.
20 Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!
Lofvad vare Gud, den mina bön icke förkastar, eller vänder sina godhet ifrå mig.