< Zabura 64 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka ji ni, ya Allah, yayinda nake faɗin abin da yake damuna; ka tsare raina daga barazanan abokin gāba.
Au maître de Chant. Psaume de David. O Dieu, écoute ma voix, quand je fais entendre mes plaintes; défends ma vie contre un ennemi qui m'épouvante;
2 Ka ɓoye ni daga ƙulle-ƙullen mugaye, daga daure dauren wannan taro masu aikata mugunta.
protège-moi contre les complots des malfaiteurs, contre la troupe soulevée des hommes iniques,
3 Sukan wāsa harsunansu kamar takuba su harba kalmominsu kamar kibiyoyi masu kisa.
qui aiguisent leurs langues comme un glaive, qui préparent leurs flèches — leur parole amère! —
4 Sukan yin kwanto su harbi marar laifi; sukan yi harbi nan da nan, ba tsoro.
pour les décocher dans l'ombre contre l'innocent; ils les décochent contre lui à l'improviste, sans rien craindre.
5 Sukan ƙarfafa juna a mugayen ƙulle-ƙullensu, sukan yi magana yadda za su ɓoye tarkunansu; su ce, “Wa zai gan su?”
Ils s'affermissent dans leurs desseins pervers, ils se concertent pour tendre leurs pièges; ils disent: " Qui les verra? "
6 Sukan yi ƙulle-ƙullen rashin adalci su ce, “Mun gama ƙulla cikakkiyar maƙarƙashiya tsab!” Zuciyar mutum da tunaninsa, suna da wuyar ganewa.
Ils ne méditent que forfaits: " Nous sommes prêts, disent-ils, notre plan est bien dressé. " L'intérieur de l'homme et son cœur sont un abîme!
7 Amma Allah zai harbe su da kibiyoyi; nan da nan za a buge su su fāɗi.
Mais Dieu a lancé sur eux ses traits: soudain les voilà blessés!
8 Zai juya harshensu a kansu yă kuma kawo su ga hallaka; duk waɗanda suka gan su za su kaɗa kai, suna musu ba’a.
On les jette par terre; les traits de leur langue retombent sur eux! Tous ceux qui les voient branlent la tête!
9 Dukan mutane za su ji tsoro; za su yi shelar ayyukan Allah su kuma yi tunanin abin da ya aikata.
Tous les hommes sont saisis de crainte, ils publient l'œuvre de Dieu, ils comprennent ce qu'il a fait.
10 Bari masu adalci su yi farin ciki a cikin Ubangiji su kuma nemi mafaka a gare shi; bari dukan masu gaskiya a zuciya su yabe shi!
Le juste se réjouit en Yahweh et se confie en lui, tous ceux qui ont le cœur droit se glorifient.

< Zabura 64 >