< Zabura 61 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka ji kukata, ya Allah; ka saurari addu’ata.
To him that excelleth on Neginoth. A Psalme of David. Heare my cry, O God: giue eare vnto my prayer.
2 Daga iyakar duniya na yi kira gare ka, na yi kira yayinda zuciyata ta karai; ka bishe ni zuwa dutsen da ya fi ni tsayi.
From the endes of the earth will I crye vnto thee: when mine heart is opprest, bring me vpon the rocke that is higher then I.
3 Gama kai ne mafakata, hasumiya mai ƙarfi gāba da maƙiyi.
For thou hast bene mine hope, and a strong tower against the enemie.
4 Ina marmari in zauna a tentinka har abada in sami mafaka a cikin inuwar fikafikanka. (Sela)
I will dwell in thy Tabernacle for euer, and my trust shall be vnder the couering of thy wings. (Selah)
5 Gama ka ji alkawarina, ya Allah; ka ba ni gādo na waɗanda suke tsoron sunanka.
For thou, O God, hast heard my desires: thou hast giuen an heritage vnto those that feare thy Name.
6 Ka ƙara kwanakin ran sarki, shekarunsa su kasance a zamanai masu yawa.
Thou shalt giue the King a long life: his yeeres shalbe as many ages.
7 Bari yă yi mulki a gaban Allah har abada; ka sa ƙaunarka da amincinka su tsare shi.
Hee shall dwell before God for euer: prepare mercie and faithfulnes that they may preserue him.
8 Sa’an nan zan riƙa rera yabo ga sunanka in kuma cika alkawarina kowace rana.
So will I alway sing prayse vnto thy Name in performing dayly my vowes.