< Zabura 59 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da Shawulu ya aiki mutane su yi tsaron gidan Dawuda don yă kashe shi. Ka cece ni daga abokan gābana, ya Allah; ka tsare ni daga waɗanda suka tayar mini.
Müzik şefi için - “Yok Etme” makamında Davut'un Miktamı - Saul'un Davut'u öldürtmek için adam gönderip evini gözetlediği zaman Kurtar beni düşmanlarımdan, ey Tanrım, Kalem ol hasımlarıma karşı.
2 Ka kuɓutar da ni daga masu aikata mugunta ka kuma cece ni daga masu kisa.
Kurtar beni suç işleyenlerden, Uzak tut kanlı katillerden.
3 Duba yadda suka kwanta suna jirana! Mugaye suna ƙulle-ƙullen gāba da ni ba saboda wani dalili ko na yi wa wani zunubi ba, ya Ubangiji.
Bak, canımı almak için pusu kuruyorlar, Güçlüler bana karşı birleşiyorlar, Oysa başkaldırmadım, günahım yok, ya RAB.
4 Ban yi wani laifi ba, duk da haka suna a shirye su fāɗa mini. Tashi ka taimake ni; dubi halin da nake ciki!
Suç işlemediğim halde, Koşuşup hazırlanıyorlar. Kalk bana yardım etmek için, halime bak!
5 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, ka tashi ka hukunta dukan al’ummai; kada ka nuna jinƙai ga mugaye maciya amana. (Sela)
Sen, ya RAB, Her Şeye Egemen Tanrı, İsrail'in Tanrısı, Uyan bütün ulusları cezalandırmak için, Acıma bu suçlu hainlere! (Sela)
6 Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
Akşam döner, köpek gibi hırlayıp Sinsi sinsi kenti dolaşırlar.
7 Dubi abin da suke tofawa daga bakunansu, suna tofar da takuba daga leɓunansu, suna cewa, “Wa zai ji mu?”
Bak, neler dökülür ağızlarından, Kılıç çıkar dudaklarından. “Kim duyacak?” derler.
8 Amma kai, ya Ubangiji, kakan yi musu dariya; kana yi wa dukan waɗannan al’ummai ba’a.
Ama sen onlara gülersin, ya RAB, Bütün uluslarla eğlenirsin.
9 Ya ƙarfina, na dogara gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata,
Gücüm sensin, seni gözlüyorum, Çünkü kalemsin, ey Tanrı.
10 Allah mai ƙaunata. Allah zai sha gabana zai kuma sa in yi dariya a kan waɗanda suke magana marar kyau a kaina.
Tanrım sevgisiyle karşılar beni, Bana düşmanlarımın yıkımını gösterir.
11 Amma kada ka kashe su, ya Ubangiji garkuwarmu, in ba haka mutanena za su manta. Cikin ikonka ka sa su yi ta yawo barkatai, ka kuma kawar da su.
Onları öldürme, yoksa halkım unutur, Gücünle dağıt ve alçalt onları, Ya Rab, kalkanımız bizim.
12 Saboda zunuban bakunansu, saboda maganganun leɓunansu, bari a kama su cikin fariyarsu. Saboda zage-zage da ƙarairayin da suke yi,
Ağızlarının günahı, dudaklarından çıkan söz yüzünden, Gururlarının tuzağına düşsünler. Okudukları lanet, söyledikleri yalan yüzünden
13 ka cinye su da hasala, ka cinye su sarai. Sa’an nan za a sani a iyakar duniya cewa Allah yana mulki a bisa Yaƙub. (Sela)
Yok et onları gazabınla, yok et, tükensinler; Bilsinler ki, Tanrı'nın Egemenliği Yakup soyundan Yeryüzünün ucuna kadar ulaşır. (Sela)
14 Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
Akşam döner, köpek gibi hırlayıp Sinsi sinsi kenti dolaşırlar.
15 Suna ta yawo neman abinci su kuwa yi haushi in ba su ƙoshi ba.
Yiyecek bulmak için gezerler, Doymazlarsa ulurlar.
16 Amma zan rera game da ƙarfinka, da safe zan rera game da ƙaunarka; gama kai ne mafakata, kagarata a lokacin wahala.
Bense gücün için sabah ezgiler söyleyecek, Sevgini sevinçle dile getireceğim. Çünkü sen bana kale, Sıkıntılı günümde sığınak oldun.
17 Ya ƙarfina, na rera yabo gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata, Allah mai ƙaunata.
Gücüm sensin, seni ilahilerle öveceğim, Çünkü kalem, beni seven Tanrı sensin.

< Zabura 59 >