< Zabura 59 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da Shawulu ya aiki mutane su yi tsaron gidan Dawuda don yă kashe shi. Ka cece ni daga abokan gābana, ya Allah; ka tsare ni daga waɗanda suka tayar mini.
Deliver me from my enemies, O my God: defend me from them that rise up against me.
2 Ka kuɓutar da ni daga masu aikata mugunta ka kuma cece ni daga masu kisa.
Deliver me from the workers of iniquity, and save me from bloody men.
3 Duba yadda suka kwanta suna jirana! Mugaye suna ƙulle-ƙullen gāba da ni ba saboda wani dalili ko na yi wa wani zunubi ba, ya Ubangiji.
For, see, they lie in wait for my soul: the mighty are gathered against me; not for my transgression, nor for my sin, O LORD.
4 Ban yi wani laifi ba, duk da haka suna a shirye su fāɗa mini. Tashi ka taimake ni; dubi halin da nake ciki!
They run and prepare themselves without my fault: awake to help me, and behold.
5 Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, ka tashi ka hukunta dukan al’ummai; kada ka nuna jinƙai ga mugaye maciya amana. (Sela)
You therefore, O LORD God of hosts, the God of Israel, awake to visit all the heathen: be not merciful to any wicked transgressors. (Selah)
6 Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
They return at evening: they make a noise like a dog, and go round about the city.
7 Dubi abin da suke tofawa daga bakunansu, suna tofar da takuba daga leɓunansu, suna cewa, “Wa zai ji mu?”
Behold, they belch out with their mouth: swords are in their lips: for who, say they, does hear?
8 Amma kai, ya Ubangiji, kakan yi musu dariya; kana yi wa dukan waɗannan al’ummai ba’a.
But you, O LORD, shall laugh at them; you shall have all the heathen in derision.
9 Ya ƙarfina, na dogara gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata,
Because of his strength will I wait on you: for God is my defense.
10 Allah mai ƙaunata. Allah zai sha gabana zai kuma sa in yi dariya a kan waɗanda suke magana marar kyau a kaina.
The God of my mercy shall prevent me: God shall let me see my desire on my enemies.
11 Amma kada ka kashe su, ya Ubangiji garkuwarmu, in ba haka mutanena za su manta. Cikin ikonka ka sa su yi ta yawo barkatai, ka kuma kawar da su.
Slay them not, lest my people forget: scatter them by your power; and bring them down, O Lord our shield.
12 Saboda zunuban bakunansu, saboda maganganun leɓunansu, bari a kama su cikin fariyarsu. Saboda zage-zage da ƙarairayin da suke yi,
For the sin of their mouth and the words of their lips let them even be taken in their pride: and for cursing and lying which they speak.
13 ka cinye su da hasala, ka cinye su sarai. Sa’an nan za a sani a iyakar duniya cewa Allah yana mulki a bisa Yaƙub. (Sela)
Consume them in wrath, consume them, that they may not be: and let them know that God rules in Jacob to the ends of the earth. (Selah)
14 Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
And at evening let them return; and let them make a noise like a dog, and go round about the city.
15 Suna ta yawo neman abinci su kuwa yi haushi in ba su ƙoshi ba.
Let them wander up and down for meat, and grudge if they be not satisfied.
16 Amma zan rera game da ƙarfinka, da safe zan rera game da ƙaunarka; gama kai ne mafakata, kagarata a lokacin wahala.
But I will sing of your power; yes, I will sing aloud of your mercy in the morning: for you have been my defense and refuge in the day of my trouble.
17 Ya ƙarfina, na rera yabo gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata, Allah mai ƙaunata.
To you, O my strength, will I sing: for God is my defense, and the God of my mercy.

< Zabura 59 >