< Zabura 58 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Ku masu mulki tabbatacce kuna magana daidai? Kuna yin shari’a daidai a cikin mutane?
Do you indeed speak righteousness, O congregation? do you judge uprightly, O you sons of men?
2 Sam, a zuciyarku kuna ƙirƙiro rashin adalci, da hannuwanku kuma kuna tā da hargitsi a duniya.
Yes, in heart you work wickedness; you weigh the violence of your hands in the earth.
3 Kai, tun haihuwa mugaye sukan kauce; daga cikin ciki, su lalatattu ne maƙaryata.
The wicked are estranged from the womb: they go astray as soon as they be born, speaking lies.
4 Dafinsu ya yi kamar dafin maciji, kamar na gamsheƙan da ya toshe kunnuwansa,
Their poison is like the poison of a serpent: they are like the deaf adder that stops her ear;
5 da ba ya jin muryar gardi, kome dabarar gwanin mai waƙar zai zama.
Which will not listen to the voice of charmers, charming never so wisely.
6 Ka kakkarya haƙoran a bakunansu, ya Allah; ka yayyage fiƙoƙin zakoki, ya Ubangiji!
Break their teeth, O God, in their mouth: break out the great teeth of the young lions, O LORD.
7 Bari su ɓace kamar ruwa mai wucewa; sa’ad da suka ja bakansu, bari kibiyoyinsu su murtsuke.
Let them melt away as waters which run continually: when he bends his bow to shoot his arrows, let them be as cut in pieces.
8 Kamar katantanwun da suke narkewa yayinda suke tafiya, kamar jinjirin da aka haifa matacce, kada su ga hasken rana.
As a snail which melts, let every one of them pass away: like the untimely birth of a woman, that they may not see the sun.
9 Kafin tukwanenka su ji zafin ƙayayyuwa, ko su kore ne ko busasshe, za a shafe mugaye.
Before your pots can feel the thorns, he shall take them away as with a whirlwind, both living, and in his wrath.
10 Masu adalci za su yi murna sa’ad da aka rama musu, sa’ad da suka wanke ƙafafunsu cikin jinin mugaye.
The righteous shall rejoice when he sees the vengeance: he shall wash his feet in the blood of the wicked.
11 Sa’an nan mutane za su ce, “Tabbatacce har yanzu ana sāka wa adalai; tabbatacce akwai Allahn da yake shari’anta duniya.”
So that a man shall say, Truly there is a reward for the righteous: truly he is a God that judges in the earth.

< Zabura 58 >