< Zabura 57 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da ya gudu daga Shawulu zuwa cikin kogo. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, ka yi mini jinƙai, gama a gare ka raina yake samun mafaka. Zan sami mafaka a inuwar fikafikanka sai masifar ta wuce.
For the Leader; Al-tashheth. A Psalm of David; Michtam; when he fled from Saul, in the cave. Be gracious unto me, O God, be gracious unto me, for in Thee hath my soul taken refuge; yea, in the shadow of Thy wings will I take refuge, until calamities be overpast.
2 Na yi kuka ga Allah Mafi Ɗaukaka, ga Allah, wanda yake cika manufarsa gare ni.
I will cry unto God Most high; unto God that accomplisheth it for me.
3 Ya aika daga sama ya kuwa cece ni, yana tsawata wa waɗanda suke fafarata da zafi; (Sela) Allah yakan aika da ƙaunarsa da amincinsa.
He will send from heaven, and save me, when he that would swallow me up taunteth; (Selah) God shall send forth His mercy and His truth.
4 Ina tsakiyar zakoki; ina kwance a cikin namun jeji masu cin mutane, mutanen da haƙoransu masu ne da kuma kibiyoyi, waɗanda harshensu suna da kaifi kamar takobi.
My soul is among lions, I do lie down among them that are aflame; even the sons of men, whose teeth are spears and arrows, and their tongue a sharp sword.
5 Bari a ɗaukaka ka, ya Allah, bisa sammai; bari ɗaukakarka ta kasance a dukan duniya.
Be Thou exalted, O God, above the heavens; Thy glory be above all the earth.
6 Sun shimfiɗa raga don su kama ƙafafuna, damuwa ta sha ƙarfina. Sun haƙa rami a hanyata, amma su kansu suka fāɗa a cikinta. (Sela)
They have prepared a net for my steps, my soul is bowed down; they have digged a pit before me, they are fallen into the midst thereof themselves. (Selah)
7 Zuciyata tana nan daram, ya Allah, zuciyata tana nan daram; zan rera in kuma yi kaɗe-kaɗe.
My heart is stedfast, O God, my heart is stedfast; I will sing, yea, I will sing praises.
8 Ka farka, raina! Ku farka, garaya da molo! Zan sa safe yă farka.
Awake, my glory; awake, psaltery and harp; I will awake the dawn.
9 Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai a cikin mutane.
I will give thanks unto Thee, O Lord, among the peoples; I will sing praises unto Thee among the nations.
10 Gama ƙaunarka mai girma ce, tana kaiwa sammai; amincinka na kaiwa sarari.
For Thy mercy is great unto the heavens, and Thy truth unto the skies.
11 Bari a ɗaukaka ka, ya Allah, bisa sammai; bari ɗaukakarka ta kasance a dukan duniya.
Be Thou exalted, O God, above the heavens; Thy glory be above all the earth.