< Zabura 56 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da murya “Kurciya a Itatuwan Oak Mai Nisa.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da Filistiyawa suka kama shi a birnin Gat. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, gama mutane sun tasar mini da zafi; dukan yini suna matsa harinsu.
Au chef des chantres. Sur “Colombe des térébinthes lointains”. Hymne de David. Lorsque les Philistins le saisirent à Gath. Aie pitié de moi, ô Dieu! Car des hommes me harcèlent; Tout le jour ils me font la guerre, ils me tourmentent.
2 Masu ɓata sunana suna bina dukan yini; da yawa suna kai mini hari cikin fariyarsu.
Tout le jour mes adversaires me harcèlent; Ils sont nombreux, ils me font la guerre comme des hautains.
3 Sa’ad da nake tsoro, zan dogara gare ka.
Quand je suis dans la crainte, En toi je me confie.
4 Ga Allah wanda maganarsa nake yabo ga Allah na dogara; ba zan ji tsoro ba. Me mutum mai mutuwa zai yi mini?
Je me glorifierai en Dieu, en sa parole; Je me confie en Dieu, je ne crains rien: Que peuvent me faire des hommes?
5 Dukan yini sun yi ta juya maganata; kullum suna ƙulle-ƙulle su cuce ni.
Sans cesse ils portent atteinte à mes droits, Ils n’ont à mon égard que de mauvaises pensées.
6 Sun haɗa baki, sun ɓoye, suna kallon takawata suna a shirye su ɗauki raina.
Ils complotent, ils épient, ils observent mes traces, Parce qu’ils en veulent à ma vie.
7 Sam, kada ka bari su kuɓuce; cikin fushinka, ya Allah, ka saukar da al’ummai.
C’est par l’iniquité qu’ils espèrent échapper: Dans ta colère, ô Dieu, précipite les peuples!
8 Ka lissafta makokina; ka jera hawayena a littafinka, ba a rubuce suke a cikin littafinka ba?
Tu comptes les pas de ma vie errante; Recueille mes larmes dans ton outre: Ne sont-elles pas inscrites dans ton livre?
9 Ta haka abokan gābana za su juya da baya sa’ad da na nemi taimako. Ta haka zan san cewa Allah yana tare da ni.
Mes ennemis reculent, au jour où je crie; Je sais que Dieu est pour moi.
10 Ga Allah, wanda nake yabon maganarsa, ga Ubangiji, wanda nake yabon maganarsa,
Je me glorifierai en Dieu, en sa parole; Je me glorifierai en l’Éternel, en sa parole;
11 ga Allah na dogara; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai iya yi mini?
Je me confie en Dieu, je ne crains rien: Que peuvent me faire des hommes?
12 Ina ƙarƙashin alkawari gare ka, ya Allah; zan miƙa hadayuna na godiya gare ka.
O Dieu! Je dois accomplir les vœux que je t’ai faits; Je t’offrirai des actions de grâces.
13 Gama ka cece ni daga mutuwa da kuma ƙafafun daga tuntuɓe, don in yi tafiya a gaban Allah cikin hasken rai.
Car tu as délivré mon âme de la mort, Tu as garanti mes pieds de la chute, Afin que je marche devant Dieu, à la lumière des vivants.

< Zabura 56 >