< Zabura 53 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat. Wani maskil na Dawuda. Wawa ne kawai yakan ce a zuciyarsa, “Ba Allah.” Sun lalace, kuma hanyoyinsu ba su da kyau; babu wani mai aikata abu mai kyau.
En undervisning Davids, i chorenom ymsom till att föresjunga. De galne säga i sitt hjerta: Det är ingen Gud till; de doga intet, och äro en styggelse vordne uti deras onda väsende; ingen är som godt gör.
2 Allah yana duba daga sama a kan’ya’yan mutane yă ga ko akwai wani wanda ya gane, wani wanda yake neman Allah.
Gud såg af himmelen uppå menniskors barn, att han måtte se, om der någor förståndig vore, den efter Gud frågade.
3 Kowa ya kauce, gaba ɗaya sun lalace; babu guda da yake aikata abu mai kyau, babu ko ɗaya.
Men de äro alle affallne, och allesammans odugelige; der är ingen, som godt gör, ja, icke en.
4 Masu aikata mugunta ba sa taɓa koyo? Suna cin mutanena kamar yadda ake cin burodi, ba sa kuma kira ga Allah.
Vilja då de ogerningsmän icke låta säga sig, de der mitt folk fräta, på det de skola föda sig? Gud åkalla de intet.
5 Ga shi fa, sun firgita don tsoro, ko da yake babu dalilin tsoro, gama Allah zai watsar da ƙasusuwan masu ƙinsa, za su sha kunya, gama Allah ya ƙi su.
Men der frukta de sig, der intet fruktande är; ty Gud förskingrar de plågares ben. Du gör dem till skam, ty Gud förmår dem.
6 Kash, da ceton Isra’ila zai fito daga Sihiyona mana! Sa’ad da Allah ya sāke arzuta mutanensa, bari Yaƙub yă yi farin ciki Isra’ila kuma yă yi murna!
Ack, att den hjelp utaf Zion öfver Israel komma måtte, och Gud sitt fångna folk förlöste; så skulle Jacob fröjda sig, och Israel glad vara.

< Zabura 53 >