< Zabura 50 >

1 Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
A psalm of Asaph. The Lord, the Almighty God, speaks! He summons everyone on earth, from the east to the west.
2 Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
God shines out of Mount Zion, perfect in beauty.
3 Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
Our God arrives, and does not stay quiet. Fire flames before him, burning everything up; a violent storm rages around him.
4 Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
He summons the heavens above and the earth to witness the judgment of his people.
5 “Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
“Bring me those who trust in me—those who confirmed the agreement with me through sacrifice.”
6 Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
The heavens declare his decisions are right, for God himself is the judge. (Selah)
7 “Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
“My people, listen to what I have to say. I am bringing charges against you, Israel. I am God, your God!
8 Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
I'm not complaining about your sacrifices or burnt offerings that you offer all the time.
9 Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
I do not require bulls from your barns or goats from your pens,
10 gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
for I own all the animals of the forest, and the cattle on a thousand hills belong to me.
11 Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
I know every bird of the mountains; all living things in the fields are mine.
12 Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
If I were hungry, I wouldn't tell you, for the earth and everything in it are mine.
13 Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
Do I eat the flesh of bulls or drink the blood of goats?
14 “Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
Give an offering of thanks to God; keep the promises you made to the Most High,
15 ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
and call on me when you're in trouble. I will rescue you, and you will thank me.”
16 Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
But to the wicked God says, “What's the point of mechanically repeating my laws or making empty promises about obeying the agreement?
17 Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
You hate my discipline, and you toss my words away, leaving them behind you.
18 Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
When you see people stealing, you admire them; you associate with adulterers.
19 Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
With your mouth you say evil things; you use your tongue to spread lies.
20 Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
You sit there and speak against your brother, slandering your own mother's son.
21 Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
I kept quiet when you did these things. You thought I was someone just like you. But now I confront you, and bring my charges against you.
22 “Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
Think again, you people who dismiss God, or I will tear you apart, and no-one will be able to save you.
23 Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”
But those who give an offering of thanks honor me, and to those who follow the right I will show them the salvation of God.”

< Zabura 50 >