< Zabura 49 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku ji wannan, dukanku mutane; ku saurara, dukanku waɗanda suke zama a wannan duniya,
Salmo para o regente, dos filhos de Coré: Ouvi isto, vós todos os povos; dai ouvidos, todos os moradores do mundo;
2 babba da yaro mai arziki da talaka.
vós, povo, filhos dos homens, tanto os ricos como os pobres.
3 Bakina zai yi maganar hikima; magana daga zuciyata za tă ba da ganewa.
Minha boca falará da sabedoria; e o pensamento do meu coração [estará cheio de] entendimento.
4 Zan juye kunnena ga karin magana; da garaya zan ƙarfafa kacici-kacicina.
Inclinarei meus ouvidos a uma parábola; ao [som] da harpa declararei o meu enigma.
5 Don me zan ji tsoro sa’ad da mugayen kwanaki suka zo, sa’ad da mugaye masu ruɗu suka kewaye ni,
Por que temeria eu nos dias do mal, [quando] a maldade dos meus adversários me cercar?
6 waɗanda suka dogara ga arzikinsu suna kuma fariya a kan yawan arzikinsu?
Eles confiam em seus bens, e se orgulham da abundância de suas riquezas.
7 Ba wani da zai iya ceton ran wani ko yă ba wa Allah kuɗin fansa saboda shi,
Mas ninguém pode livrar o seu irmão, nem pagar a Deus o seu resgate,
8 kuɗin fansa domin rai yana da tsada, babu abin da za a biya da ya taɓa isa,
porque a redenção da sua alma é caríssima, e sempre será insuficiente
9 da zai sa yă ci gaba da rayuwa har abada yă hana shi shigan kabari yă ruɓa.
para viver eternamente, e jamais ver a cova.
10 Gama kowa na iya ganin masu hikima na mutuwa; wawaye da marasa azanci su ma kan hallaka su bar wa waɗansu arzikinsu.
Pois se vê que os sábios morrem, que o tolo e o bruto igualmente perecem; e deixam suas riquezas a outros.
11 Kaburburansu za su ci gaba da zama gidajensu har abada, Can za su kasance har zamanai marasa ƙarewa, ko da yake sun ba wa filaye sunayen kansu.
Seu pensamento interior é que suas casas serão perpétuas, que suas moradas durarão de geração em geração; dão às terras os seus próprios nomes.
12 Amma mutum, kome arzikinsa, ba ya dawwama; shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
Mas o ser humano, ainda que em honra, não dura para sempre; semelhante é aos animais, que perecem.
13 Wannan ne ƙaddarar waɗanda suke dogara a kansu, da kuma ta mabiyansu, waɗanda suka tabbatar da faɗinsu. (Sela)
Este é o caminho dos tolos e dos seus seguidores, que se agradam de suas palavras. (Selá)
14 Kamar tumaki an ƙaddara su ga kabari; za su kuwa zama abincin mutuwa amma masu gaskiya za su yi mulki a kansu da safe. Kamanninsu za su ruɓe a cikin kabari, nesa da gidajensu masu tsada. (Sheol h7585)
São como ovelhas levados ao Xeol; a morte se alimentará deles. Os corretos os dominarão pela manhã, e sua beleza será consumida no Xeol, longe de sua morada. (Sheol h7585)
15 Amma Allah zai ceci raina daga kabari; tabbatacce zai ɗauke ni zuwa wurinsa. (Sela) (Sheol h7585)
Mas Deus resgatará a minha alma da violência do mundo dos mortos, pois ele me tomará [consigo]. (Selá) (Sheol h7585)
16 Kada ka razana da yawa sa’ad da mutum ya yi arziki sa’ad da darajar gidansa ta ƙaru;
Não temas quando um homem enriquece, quando a glória de sua casa se engrandece.
17 gama ba zai ɗauki kome tare da shi sa’ad da ya mutu ba, darajarsa ba za tă gangara tare da shi ba.
Pois ele, quando morrer, nada levará; nem sua glória o seguirá abaixo.
18 Ko da yake yayinda yake a raye ya ɗauka kansa mai albarka ne, mutane kuma sun yabe ka sa’ad da kake cin nasara,
Ainda que, em vida, tenha pronunciado a si mesmo a bênção “Louvam-te ao fazeres o bem a ti”,
19 zai gamu da tsarar kakanninsa, waɗanda ba za su taɓa ganin hasken rayuwa ba.
ele, porém, se juntará à geração de seus pais; nunca mais verão a luz.
20 Mutumin da yake da arziki ba tare da ganewa ba shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
O homem em posição de honra que não tem entendimento é semelhante aos animais, que perecem.

< Zabura 49 >