< Zabura 49 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku ji wannan, dukanku mutane; ku saurara, dukanku waɗanda suke zama a wannan duniya,
Til songmeisteren; av Korahs born; ein salme. Høyr dette, alle folk, vend øyra til, alle de som bur i verdi,
2 babba da yaro mai arziki da talaka.
både låge og høge, rik og fatig, alle saman!
3 Bakina zai yi maganar hikima; magana daga zuciyata za tă ba da ganewa.
Min munn skal tala visdom, og det som mitt hjarta tenkjer upp, er vit.
4 Zan juye kunnena ga karin magana; da garaya zan ƙarfafa kacici-kacicina.
Eg vil bøygja mitt øyra til fyndord, eg vil lata upp mi gåta til harpeljod.
5 Don me zan ji tsoro sa’ad da mugayen kwanaki suka zo, sa’ad da mugaye masu ruɗu suka kewaye ni,
Kvi skal eg ottast i dei vonde dagar, når vondskap av mine forfylgjarar kringset meg,
6 waɗanda suka dogara ga arzikinsu suna kuma fariya a kan yawan arzikinsu?
dei som set si lit til sitt gods og rosar seg av sin store rikdom?
7 Ba wani da zai iya ceton ran wani ko yă ba wa Allah kuɗin fansa saboda shi,
Ein mann kann ikkje løysa ut ein bror, kann ikkje gjeva Gud løysepengar for honom
8 kuɗin fansa domin rai yana da tsada, babu abin da za a biya da ya taɓa isa,
- utløysingi av deira liv er for dyr, og han let det vera til æveleg tid -
9 da zai sa yă ci gaba da rayuwa har abada yă hana shi shigan kabari yă ruɓa.
so han skulde halda ved å liva for alltid og ikkje sjå gravi.
10 Gama kowa na iya ganin masu hikima na mutuwa; wawaye da marasa azanci su ma kan hallaka su bar wa waɗansu arzikinsu.
Nei, han må sjå: Vismenner døyr, dåre og fåviting gjeng burt alle saman og let sitt gods etter seg til andre.
11 Kaburburansu za su ci gaba da zama gidajensu har abada, Can za su kasance har zamanai marasa ƙarewa, ko da yake sun ba wa filaye sunayen kansu.
Deira inste tanke er at deira hus skal standa æveleg, deira bustader frå ætt til ætt; dei kallar sin jorder etter sine namn.
12 Amma mutum, kome arzikinsa, ba ya dawwama; shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
Men eit menneskje i høg vyrdnad vert ikkje verande; han er lik dyri, dei må tagna.
13 Wannan ne ƙaddarar waɗanda suke dogara a kansu, da kuma ta mabiyansu, waɗanda suka tabbatar da faɗinsu. (Sela)
So gjeng det deim som er fulle av tru til seg sjølve, og etter deim fylgjer dei som likar deira tale. (Sela)
14 Kamar tumaki an ƙaddara su ga kabari; za su kuwa zama abincin mutuwa amma masu gaskiya za su yi mulki a kansu da safe. Kamanninsu za su ruɓe a cikin kabari, nesa da gidajensu masu tsada. (Sheol h7585)
Som sauer vert dei førde ned i helheimen, dauden gjæter deim, og dei trurøkne tred deim ned, når morgonen renn; og deira skapnad vert øydelagd av helheimen, so dei hev ingen heimstad lenger. (Sheol h7585)
15 Amma Allah zai ceci raina daga kabari; tabbatacce zai ɗauke ni zuwa wurinsa. (Sela) (Sheol h7585)
Men Gud skal løysa ut mi sjæl or handi på helheimen; for han skal taka meg til seg. (Sela) (Sheol h7585)
16 Kada ka razana da yawa sa’ad da mutum ya yi arziki sa’ad da darajar gidansa ta ƙaru;
Ottast ikkje når ein mann vert rik, når hans hus kjem til stor æra!
17 gama ba zai ɗauki kome tare da shi sa’ad da ya mutu ba, darajarsa ba za tă gangara tare da shi ba.
For han skal ingen ting taka med seg når han døyr; hans æra skal ikkje fara ned etter honom.
18 Ko da yake yayinda yake a raye ya ɗauka kansa mai albarka ne, mutane kuma sun yabe ka sa’ad da kake cin nasara,
Um han og velsignar si sjæl i si livstid, og dei prisar deg for di du gjer deg gode dagar,
19 zai gamu da tsarar kakanninsa, waɗanda ba za su taɓa ganin hasken rayuwa ba.
so skal du då koma til di fedreætt, dei som ikkje ser ljoset i all æva.
20 Mutumin da yake da arziki ba tare da ganewa ba shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
Eit menneskje i høg vyrdnad, som ikkje hev vit, vert lik dyri; dei må tagna.

< Zabura 49 >