< Zabura 49 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku ji wannan, dukanku mutane; ku saurara, dukanku waɗanda suke zama a wannan duniya,
In finem, filiis Core. Psalmus. [Audite hæc, omnes gentes; auribus percipite, omnes qui habitatis orbem:
2 babba da yaro mai arziki da talaka.
quique terrigenæ et filii hominum, simul in unum dives et pauper.
3 Bakina zai yi maganar hikima; magana daga zuciyata za tă ba da ganewa.
Os meum loquetur sapientiam, et meditatio cordis mei prudentiam.
4 Zan juye kunnena ga karin magana; da garaya zan ƙarfafa kacici-kacicina.
Inclinabo in parabolam aurem meam; aperiam in psalterio propositionem meam.
5 Don me zan ji tsoro sa’ad da mugayen kwanaki suka zo, sa’ad da mugaye masu ruɗu suka kewaye ni,
Cur timebo in die mala? iniquitas calcanei mei circumdabit me.
6 waɗanda suka dogara ga arzikinsu suna kuma fariya a kan yawan arzikinsu?
Qui confidunt in virtute sua, et in multitudine divitiarum suarum, gloriantur.
7 Ba wani da zai iya ceton ran wani ko yă ba wa Allah kuɗin fansa saboda shi,
Frater non redimit, redimet homo: non dabit Deo placationem suam,
8 kuɗin fansa domin rai yana da tsada, babu abin da za a biya da ya taɓa isa,
et pretium redemptionis animæ suæ. Et laborabit in æternum;
9 da zai sa yă ci gaba da rayuwa har abada yă hana shi shigan kabari yă ruɓa.
et vivet adhuc in finem.
10 Gama kowa na iya ganin masu hikima na mutuwa; wawaye da marasa azanci su ma kan hallaka su bar wa waɗansu arzikinsu.
Non videbit interitum, cum viderit sapientes morientes: simul insipiens et stultus peribunt. Et relinquent alienis divitias suas,
11 Kaburburansu za su ci gaba da zama gidajensu har abada, Can za su kasance har zamanai marasa ƙarewa, ko da yake sun ba wa filaye sunayen kansu.
et sepulchra eorum domus illorum in æternum; tabernacula eorum in progenie et progenie: vocaverunt nomina sua in terris suis.
12 Amma mutum, kome arzikinsa, ba ya dawwama; shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
Et homo, cum in honore esset, non intellexit. Comparatus est jumentis insipientibus, et similis factus est illis.
13 Wannan ne ƙaddarar waɗanda suke dogara a kansu, da kuma ta mabiyansu, waɗanda suka tabbatar da faɗinsu. (Sela)
Hæc via illorum scandalum ipsis; et postea in ore suo complacebunt.
14 Kamar tumaki an ƙaddara su ga kabari; za su kuwa zama abincin mutuwa amma masu gaskiya za su yi mulki a kansu da safe. Kamanninsu za su ruɓe a cikin kabari, nesa da gidajensu masu tsada. (Sheol h7585)
Sicut oves in inferno positi sunt: mors depascet eos. Et dominabuntur eorum justi in matutino; et auxilium eorum veterascet in inferno a gloria eorum. (Sheol h7585)
15 Amma Allah zai ceci raina daga kabari; tabbatacce zai ɗauke ni zuwa wurinsa. (Sela) (Sheol h7585)
Verumtamen Deus redimet animam meam de manu inferi, cum acceperit me. (Sheol h7585)
16 Kada ka razana da yawa sa’ad da mutum ya yi arziki sa’ad da darajar gidansa ta ƙaru;
Ne timueris cum dives factus fuerit homo, et cum multiplicata fuerit gloria domus ejus:
17 gama ba zai ɗauki kome tare da shi sa’ad da ya mutu ba, darajarsa ba za tă gangara tare da shi ba.
quoniam, cum interierit, non sumet omnia, neque descendet cum eo gloria ejus.
18 Ko da yake yayinda yake a raye ya ɗauka kansa mai albarka ne, mutane kuma sun yabe ka sa’ad da kake cin nasara,
Quia anima ejus in vita ipsius benedicetur; confitebitur tibi cum benefeceris ei.
19 zai gamu da tsarar kakanninsa, waɗanda ba za su taɓa ganin hasken rayuwa ba.
Introibit usque in progenies patrum suorum; et usque in æternum non videbit lumen.
20 Mutumin da yake da arziki ba tare da ganewa ba shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
Homo, cum in honore esset, non intellexit. Comparatus est jumentis insipientibus, et similis factus est illis.]

< Zabura 49 >