< Zabura 49 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku ji wannan, dukanku mutane; ku saurara, dukanku waɗanda suke zama a wannan duniya,
Til Sangmesteren. Af Koras Sønner. En Salme. Hør det, alle Folkeslag, lyt til, al Verdens Folk,
2 babba da yaro mai arziki da talaka.
baade høj og lav, baade rig og fattig!
3 Bakina zai yi maganar hikima; magana daga zuciyata za tă ba da ganewa.
Min Mund skal tale Visdom, mit Hjerte udgransker Indsigt;
4 Zan juye kunnena ga karin magana; da garaya zan ƙarfafa kacici-kacicina.
jeg bøjer mit Øre til Tankesprog, raader min Gaade til Strengeleg.
5 Don me zan ji tsoro sa’ad da mugayen kwanaki suka zo, sa’ad da mugaye masu ruɗu suka kewaye ni,
Hvorfor skulle jeg frygte i de onde Dage, naar mine lumske Fjender omringer mig med Brøde,
6 waɗanda suka dogara ga arzikinsu suna kuma fariya a kan yawan arzikinsu?
de, som stoler paa deres Gods og bryster sig af deres store Rigdom?
7 Ba wani da zai iya ceton ran wani ko yă ba wa Allah kuɗin fansa saboda shi,
Visselig, ingen kan købe sin Sjæl fri og give Gud en Løsesum
8 kuɗin fansa domin rai yana da tsada, babu abin da za a biya da ya taɓa isa,
— Prisen for hans Sjæl blev for høj, for evigt maatte han opgive det — saa han kunde blive i Live
9 da zai sa yă ci gaba da rayuwa har abada yă hana shi shigan kabari yă ruɓa.
og aldrig faa Graven at se;
10 Gama kowa na iya ganin masu hikima na mutuwa; wawaye da marasa azanci su ma kan hallaka su bar wa waɗansu arzikinsu.
nej, han skal se den; Vismænd dør, baade Daare og Taabe gaar bort. Deres Gods maa de afstaa til andre,
11 Kaburburansu za su ci gaba da zama gidajensu har abada, Can za su kasance har zamanai marasa ƙarewa, ko da yake sun ba wa filaye sunayen kansu.
deres Grav er deres Hjem for evigt, deres Bolig Slægt efter Slægt, om Godser end fik deres Navn.
12 Amma mutum, kome arzikinsa, ba ya dawwama; shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
Trods Herlighed bliver Mennesket ikke, han er som Dyrene, der forgaar.
13 Wannan ne ƙaddarar waɗanda suke dogara a kansu, da kuma ta mabiyansu, waɗanda suka tabbatar da faɗinsu. (Sela)
Saa gaar det dem, der tror sig trygge, saa ender det for dem, deres Tale behager. (Sela)
14 Kamar tumaki an ƙaddara su ga kabari; za su kuwa zama abincin mutuwa amma masu gaskiya za su yi mulki a kansu da safe. Kamanninsu za su ruɓe a cikin kabari, nesa da gidajensu masu tsada. (Sheol h7585)
I Dødsriget drives de ned som Faar, deres Hyrde skal Døden være; de oprigtige træder paa dem ved Gry, deres Skikkelse gaar Opløsning i Møde, Dødsriget er deres Bolig. (Sheol h7585)
15 Amma Allah zai ceci raina daga kabari; tabbatacce zai ɗauke ni zuwa wurinsa. (Sela) (Sheol h7585)
Men Gud udløser min Sjæl af Dødsrigets Haand, thi han tager mig til sig. (Sela) (Sheol h7585)
16 Kada ka razana da yawa sa’ad da mutum ya yi arziki sa’ad da darajar gidansa ta ƙaru;
Frygt ej, naar en Mand bliver rig, naar hans Huses Herlighed øges;
17 gama ba zai ɗauki kome tare da shi sa’ad da ya mutu ba, darajarsa ba za tă gangara tare da shi ba.
thi intet tager han med i Døden, hans Herlighed følger ham ikke.
18 Ko da yake yayinda yake a raye ya ɗauka kansa mai albarka ne, mutane kuma sun yabe ka sa’ad da kake cin nasara,
Priser han end i Live sig selv: »De lover dig for din Lykke!« —
19 zai gamu da tsarar kakanninsa, waɗanda ba za su taɓa ganin hasken rayuwa ba.
han vandrer til sine Fædres Slægt, der aldrig faar Lyset at skue.
20 Mutumin da yake da arziki ba tare da ganewa ba shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
Den, som lever i Herlighed, men uden Forstand, han er som Dyrene, der forgaar.

< Zabura 49 >