< Zabura 47 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku tafa hannuwanku, dukanku al’ummai; ku yi sowa ga Allah da muryoyin farin ciki.
¡Pueblos todos, aplaudan! ¡Aclamen a ʼElohim con voz de júbilo!
2 Ubangiji Mafi Ɗaukaka mai banmamaki ne, Sarki ne mai girma a bisa dukan duniya!
Porque Yavé el ʼElyón es temible, Rey grande sobre toda la tierra.
3 Ya rinjayi al’ummai a ƙarƙashinmu, mutane kuma a ƙarƙashin ƙafafunmu.
Él somete los pueblos a nosotros, Las naciones bajo nuestros pies.
4 Ya zaɓar mana gādonmu, abar taƙamar Yaƙub, wanda yake ƙauna. (Sela)
Él nos eligió nuestra herencia, El Esplendor de Jacob, a quien amó. (Selah)
5 Allah ya haura a cikin sowa ta farin ciki, Ubangiji ya haura a cikin ƙarar ƙahoni.
ʼElohim asciende con aclamación de júbilo, Yavé con sonido de trompeta.
6 Ku rera yabai ga Allah, ku rera yabai; ku rera yabai ga Sarkinmu, ku rera yabai.
¡Canten a ʼElohim, canten! ¡Canten a nuestro Rey, canten!
7 Gama Allah shi ne Sarkin dukan duniya; ku rera zabura ta yabo gare shi.
Porque ʼElohim es el Rey de toda la tierra. ¡Canten con entendimiento!
8 Allah yana mulki a bisa al’ummai; Allah yana zama a kan kursiyinsa mai tsarki.
¡ʼElohim reina sobre las naciones! ¡ʼElohim se sienta en su santo trono!
9 Manyan mutanen al’ummai sun taru a matsayin mutanen Allah na Ibrahim, gama sarkunan duniya na Allah ne; ana ɗaukaka shi ƙwarai.
Los jefes de las naciones se reúnen como pueblo del ʼElohim de Abraham, Porque de ʼElohim son los escudos de la tierra, Él es sumamente exaltado.