< Zabura 47 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku tafa hannuwanku, dukanku al’ummai; ku yi sowa ga Allah da muryoyin farin ciki.
Salmo para o regente, dos filhos de Coré: Vós todos os povos, batei palmas; clamai a Deus com voz de alegria.
2 Ubangiji Mafi Ɗaukaka mai banmamaki ne, Sarki ne mai girma a bisa dukan duniya!
Porque o SENHOR Altíssimo [é] temível, o grande Rei sobre toda a terra.
3 Ya rinjayi al’ummai a ƙarƙashinmu, mutane kuma a ƙarƙashin ƙafafunmu.
Ele subjugará aos povos debaixo de nós, e as nações debaixo de nossos pés.
4 Ya zaɓar mana gādonmu, abar taƙamar Yaƙub, wanda yake ƙauna. (Sela)
Ele escolhe para nós nossa herança, a glória de Jacó, a quem ele amou. (Selá)
5 Allah ya haura a cikin sowa ta farin ciki, Ubangiji ya haura a cikin ƙarar ƙahoni.
Deus sobe com gritos de alegria; o SENHOR, com voz de trombeta.
6 Ku rera yabai ga Allah, ku rera yabai; ku rera yabai ga Sarkinmu, ku rera yabai.
Cantai louvores a Deus, cantai; cantai louvores ao nosso Rei, cantai.
7 Gama Allah shi ne Sarkin dukan duniya; ku rera zabura ta yabo gare shi.
Porque Deus é o Rei de toda a terra; cantai louvores com entendimento.
8 Allah yana mulki a bisa al’ummai; Allah yana zama a kan kursiyinsa mai tsarki.
Deus reina sobre as nações; Deus se senta sobre o trono de sua santidade.
9 Manyan mutanen al’ummai sun taru a matsayin mutanen Allah na Ibrahim, gama sarkunan duniya na Allah ne; ana ɗaukaka shi ƙwarai.
Os chefes dos povos se juntaram ao povo do Deus de Abraão, porque os escudos da terra pertencem a Deus, [e] ele é muito exaltado.

< Zabura 47 >