< Zabura 46 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Bisa ga alamot Waƙa ce. Allah ne mafakarmu da ƙarfinmu, kullum yana a shirye yă taimaka a lokacin wahala.
Au chef des chantres. Par les fils de Coré. Cantique sur les Alamoth. Dieu est pour nous un abri, une force, un appui dans les tourments, facilement accessible.
2 Saboda haka ba za mu ji tsoro ba, ko da ƙasa ta girgiza duwatsu kuma suka fāɗi cikin zurfin teku,
Aussi ne craindrons-nous rien, dût la terre bouger de sa place, et les montagnes s’abîmer au sein de l’Océan;
3 ko da ruwansa suna ruri suna kumfa duwatsu kuma suna girgiza da tumbatsansu. (Sela)
dussent ses flots gronder et bouillonner, et les montagnes trembler quand il entre en fureur!
4 Akwai kogi mai rafuffukan da suke sa birnin Allah murna, tsattsarkan wuri inda Mafi Ɗaukaka ke zama.
Le fleuve…! Ses ondes réjouissent la ville de Dieu, demeure sainte du Très-Haut.
5 Allah yana cikinta, ba za tă fāɗi ba; Allah zai taimake ta da safe.
Dieu réside au milieu d’elle: elle ne sera point ébranlée, Dieu venant à son secours dès le lever de l’aurore.
6 Al’ummai suna hayaniya, mulkoki sun fāɗi; ya ɗaga muryarsa, duniya ta narke.
Les peuples s’agitent, les royaumes chancellent; il fait retentir sa voix: la terre se liquéfie!
7 Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu; Allah na Yaƙub ne kagararmu. (Sela)
L’Eternel-Cebaot est avec nous, le Dieu de Jacob est une citadelle pour nous. (Sélah)
8 Zo ku ga ayyukan Ubangiji, kangon da ya kawo a kan duniya.
Venez, contemplez les œuvres de l’Eternel, qui a opéré des ruines sur la terre!
9 Ya sa yaƙoƙi suka yi tsit ko’ina a duniya. Ya kakkarya bakkuna ya kuma ragargaza māsu, ya ƙone garkuwoyi da wuta.
Il met fin aux guerres jusqu’aux confins du globe, il brise les arcs, met en pièces les lances, et livre au feu les chars des combats.
10 “Ku natsu ku kuma san cewa ni ne Allah; za a ɗaukaka ni a cikin al’ummai, za a ɗaukaka ni cikin duniya.”
Tenez-vous cois et sachez que moi, je suis Dieu, grand parmi les peuples, grand sur la terre!
11 Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu; Allah na Yaƙub ne kagararmu. (Sela)
L’Eternel-Cebaot est avec nous, le Dieu de Jacob est une citadelle pour nous. (Sélah)

< Zabura 46 >