< Zabura 44 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
Müzik şefi için - Korahoğulları'nın Maskili Ey Tanrı, kulaklarımızla duyduk, Atalarımız anlattı bize, Neler yaptığını onların gününde, eski günlerde.
2 Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
Elinle ulusları kovdun, Ama atalarımıza yer verdin; Halkları kırdın, Ama atalarımızın yayılmasını sağladın.
3 Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
Onlar ülkeyi kılıçla kazanmadılar, Kendi bilekleriyle zafere ulaşmadılar. Senin sağ elin, bileğin, yüzünün ışığı sayesinde oldu bu; Çünkü sen onları sevdin.
4 Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
Ey Tanrı, kralım sensin, Buyruk ver de Yakup soyu kazansın!
5 Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
Senin sayende düşmanlarımızı püskürteceğiz, Senin adınla karşıtlarımızı ezeceğiz.
6 Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
Çünkü ben yayıma güvenmem, Kılıcım da beni kurtarmaz;
7 amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
Ancak sensin bizi düşmanlarımızdan kurtaran, Bizden nefret edenleri utanca boğan.
8 A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
Her gün Tanrı'yla övünür, Sonsuza dek adına şükran sunarız. (Sela)
9 Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
Ne var ki, reddettin bizi, aşağıladın, Artık ordularımızla savaşa çıkmıyorsun.
10 Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
Düşman karşısında bizi gerilettin, Bizden tiksinenler bizi soydu.
11 Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
Kasaplık koyuna çevirdin bizi, Ulusların arasına dağıttın.
12 Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
Yok pahasına sattın halkını, Üstelik satıştan hiçbir şey kazanmadan.
13 Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
Bizi komşularımızın yüzkarası, Çevremizdekilerin eğlencesi, alay konusu ettin.
14 Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
Ulusların diline düşürdün bizi, Gülüyor halklar halimize.
15 Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
Rezilliğim gün boyu karşımda, Utancımdan yerin dibine geçtim
16 saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
Hakaret ve sövgü duya duya, Öç almak isteyen düşman karşısında.
17 Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
Bütün bunlar başımıza geldi, Yine de seni unutmadık, Antlaşmana ihanet etmedik,
18 Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
Döneklik etmedik, Adımlarımız senin yolundan sapmadı.
19 Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
Oysa sen bizi ezdin, ülkemizi çakalların uğrağı ettin, Üstümüzü koyu karanlıkla örttün.
20 Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
Eğer Tanrımız'ın adını unutsaydık, Yabancı bir ilaha ellerimizi açsaydık,
21 da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
Tanrı bunu ortaya çıkarmaz mıydı? Çünkü O yürekteki gizleri bilir.
22 Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
Senin uğruna her gün öldürülüyoruz, Kasaplık koyun sayılıyoruz.
23 Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
Uyan, ya Rab! Niçin uyuyorsun? Kalk! Sonsuza dek terk etme bizi!
24 Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
Niçin yüzünü gizliyorsun? Neden mazlum halimizi, üzerimizdeki baskıyı unutuyorsun?
25 An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
Çünkü yere serildik, Bedenimiz toprağa yapıştı.
26 Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.
Kalk, yardım et bize! Kurtar bizi sevgin uğruna!

< Zabura 44 >