< Zabura 42 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Maskil ne na’Ya’yan Kora maza. Kamar yadda barewa take marmarin ruwan rafuffuka, haka raina yake marmarinka, ya Allah.
Para el músico principal. Una contemplación de los hijos de Coré. Como el ciervo que busca los arroyos de agua, por lo que mi alma suspira por ti, Dios.
2 Raina yana ƙishin Allah, Allah mai rai. Yaushe zan tafi in sadu da Allah ne?
Mi alma tiene sed de Dios, del Dios vivo. ¿Cuándo vendré a comparecer ante Dios?
3 Hawayena ne sun zama abincina dare da rana, yayinda mutane suke ce da ni dukan yini, “Ina Allahnka ɗin?”
Mis lágrimas han sido mi alimento día y noche, mientras me preguntan continuamente: “¿Dónde está tu Dios?”
4 Waɗannan abubuwa ne nakan tuna sa’ad da nake faɗin abin da yake a raina, yadda dā nakan tafi tare da taron jama’a, ina bishe su a jere zuwa gidan Allah, da sowa ta farin ciki da kuma godiya a cikin taron biki.
De esto me acuerdo, y derramo mi alma dentro de mí, cómo solía ir con la multitud, y los llevaba a la casa de Dios, con voz de alegría y alabanza, una multitud que celebra un día santo.
5 Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina? Me ya sa ka damu a cikina? Ka dogara ga Allah, gama zai sāke yabe shi, Mai Cetona da kuma Allahna.
¿Por qué te desesperas, alma mía? ¿Por qué te perturbas dentro de mí? ¡Espera en Dios! Porque aún le alabaré por la ayuda salvadora de su presencia.
6 Raina yana baƙin ciki a cikina; saboda haka zan tuna da kai daga ƙasar Urdun, a ƙwanƙolin Hermon, daga Dutsen Mizar.
Dios mío, mi alma está desesperada dentro de mí. Por eso me acuerdo de ti desde la tierra del Jordán, las alturas del Hermón, desde la colina Mizar.
7 Zurfi kan kira zurfi cikin rurin matsirgar ruwanka; dukan raƙuma da igiyoyi sun sha kaina.
Llamadas profundas al ruido de sus cascadas. Todas tus olas y tus olas me han barrido.
8 Da rana Ubangiji yakan nuna ƙaunarsa, da dare waƙarsa tana tare da ni, addu’a ga Allah na raina.
Yahvé ordenará su bondad amorosa durante el día. En la noche su canción estará conmigo: una oración al Dios de mi vida.
9 Na ce wa Allah Dutsena, “Me ya sa ka manta da ni? Me zai sa in yi ta yawo ina makoki, a danne a hannun abokin gāba?”
Preguntaré a Dios, mi roca: “¿Por qué me has olvidado? ¿Por qué voy de luto por la opresión del enemigo?”
10 Ƙasusuwana suna jin jiki da wahala yayinda maƙiyana suna mini ba’a, suna ce mini dukan yini, “Ina Allahnka ɗin?”
Como con una espada en los huesos, mis adversarios me reprochan, mientras me preguntan continuamente: “¿Dónde está tu Dios?”
11 Me ya sa kake baƙin ciki, ya raina? Me ya sa ka damu a cikina? Ka dogara ga Allah, gama zai sāke yabe shi, Mai Cetona da kuma Allahna.
¿Por quéestás desesperada, alma mía? ¿Por qué te perturbas dentro de mí? ¡Espera en Dios! Porque todavía lo alabaré, la ayuda salvadora de mi rostro, y mi Dios.