< Zabura 4 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka amsa mini sa’ad da na kira gare ka, Ya Allahna mai adalci. Ka ba ni sauƙi daga wahalata; ka ji tausayina ka kuma ji addu’ata.
למנצח בנגינות מזמור לדוד בקראי ענני אלהי צדקי בצר הרחבת לי חנני ושמע תפלתי׃
2 Har yaushe, ya ku mutane za ku mai da ɗaukakata abin kunya? Har yaushe za ku ƙaunaci ruɗu ku nemi allolin ƙarya? (Sela)
בני איש עד מה כבודי לכלמה תאהבון ריק תבקשו כזב סלה׃
3 Ku san cewa Ubangiji ya keɓe masu tsoron Allah wa kansa; Ubangiji zai ji sa’ad da na yi kira gare shi.
ודעו כי הפלה יהוה חסיד לו יהוה ישמע בקראי אליו׃
4 Cikin fushinku kada ku yi zunubi; sa’ad da kuke kan gadajenku, ku bincike zukatanku ku kuma yi shiru. (Sela)
רגזו ואל תחטאו אמרו בלבבכם על משכבכם ודמו סלה׃
5 Ku miƙa hadayun da suka dace ku kuma dogara ga Ubangiji.
זבחו זבחי צדק ובטחו אל יהוה׃
6 Yawanci suna cewa, “Wa zai yi mana alheri?” Bari hasken fuskarka yă haskaka a kanmu, ya Ubangiji.
רבים אמרים מי יראנו טוב נסה עלינו אור פניך יהוה׃
7 Ka cika zuciyata da farin ciki sa’ad da hatsinsu da sabon ruwan inabinsu ya yi yawa.
נתתה שמחה בלבי מעת דגנם ותירושם רבו׃
8 Zan kwanta in kuma yi barci lafiya, gama kai kaɗai, ya Ubangiji, kake sa mazaunina yă kasance lafiya lau.
בשלום יחדו אשכבה ואישן כי אתה יהוה לבדד לבטח תושיבני׃

< Zabura 4 >