< Zabura 4 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka amsa mini sa’ad da na kira gare ka, Ya Allahna mai adalci. Ka ba ni sauƙi daga wahalata; ka ji tausayina ka kuma ji addu’ata.
“To the chief musician on Neginoth, a psalm of David.” When I call, answer me, O God of my righteousness: amidst distress thou hast [ever] granted me enlargement; be gracious unto me, and hear my prayer.
2 Har yaushe, ya ku mutane za ku mai da ɗaukakata abin kunya? Har yaushe za ku ƙaunaci ruɗu ku nemi allolin ƙarya? (Sela)
O ye sons of men, how long shall my glory be put to shame? [how long] will ye love vanity, will ye seek for lies? (Selah)
3 Ku san cewa Ubangiji ya keɓe masu tsoron Allah wa kansa; Ubangiji zai ji sa’ad da na yi kira gare shi.
But know that the Lord hath set apart the pious for himself: the Lord will hear when I call on him.
4 Cikin fushinku kada ku yi zunubi; sa’ad da kuke kan gadajenku, ku bincike zukatanku ku kuma yi shiru. (Sela)
Tremble, and sin not: commune with your heart upon your bed, and be still (Selah)
5 Ku miƙa hadayun da suka dace ku kuma dogara ga Ubangiji.
Offer the sacrifices of righteousness, and put your trust in the Lord.
6 Yawanci suna cewa, “Wa zai yi mana alheri?” Bari hasken fuskarka yă haskaka a kanmu, ya Ubangiji.
Many say, “Who will show us happiness? Let shine brightly over us the light of thy countenance, O Lord.”
7 Ka cika zuciyata da farin ciki sa’ad da hatsinsu da sabon ruwan inabinsu ya yi yawa.
[But] thou hast placed more joy in my heart than at the time when their corn and their wine were increased.
8 Zan kwanta in kuma yi barci lafiya, gama kai kaɗai, ya Ubangiji, kake sa mazaunina yă kasance lafiya lau.
In peace, altogether, will I lay me down and sleep; for thou, Lord, alone, causest me to dwell in safety.

< Zabura 4 >