< Zabura 38 >

1 Zabura ta Dawuda. Roƙo ne. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
Un Salmo de David, pidiendo a Dios que se acuerde de él. ¡Señor, por favor no me condenes, por causa de tu enojo conmigo! ¡No me castigues con tu furia!
2 Gama kibiyoyinka sun soke ni, hannunka kuma ya fāɗo a kaina.
Tus flechas me han atravesado, tus manos han caído sobre mí.
3 Saboda hasalarka babu lafiya a jikina; ƙasusuwana ba lafiya saboda zunubina.
Por tu enojo hacia mí, ni una sola parte de mi cuerpo está sana. Estoy completamente enfermo por mis pecados.
4 Laifofina sun mamaye ni kamar nauyin da ya sha ƙarfin ɗauka.
Me estoy ahogando en culpa. La carga es muy pesada de llevar.
5 Miyakuna sun ruɓe suna kuma wari saboda wawancina na zunubi.
Mis heridas están infectadas, están comenzando a oler mal, y por culpa de mi terquedad.
6 An tanƙware ni aka kuma ƙasƙantar da ni; dukan yini ina ta kuka.
Estoy encorvado, retorcido por el dolor. Camino el día entero llorando y lamentándome.
7 Bayana yana fama da zazzaɓi; babu lafiya a jikina.
Estoy ardiendo por dentro de fiebre. Ninguna parte de mi cuerpo está sana.
8 Na gaji sharkaf an kuma ragargaza ni; ina nishi da wahala a cikin zuciyata.
Estoy muy cansado, totalmente deshecho. Siento mi corazón como ruge de angustia.
9 Dukan bukatata tana a shimfiɗe a gabanka, ya Ubangiji; ajiyar zuciyata ba ta ɓoyuwa daga gare ka.
Señor, sabes lo que quiero desesperadamente, escuchas cada respiración que tomo.
10 Zuciyata na bugu, ƙarfina kuma ya ƙare, har ma haske ya rabu da idanuna.
Mi corazón se está acelerando, dejándome sin fuerza. Mi vista está decayendo.
11 Abokaina da maƙwabtana sun guje ni saboda miyakuna; maƙwabtana ba sa zuwa kusa.
Mis amados y amigos no se me acercan porque tienen miedo de contagiarse. Incluso mi familia se ha distanciado.
12 Waɗanda suke neman raina sun sa tarkonsu, waɗanda suke so su cuce ni suna zance lalatar da ni; yini sukutum suna ƙulla mini maƙarƙashiya.
Aquellos que intentan matarme me ponen trampas. Los que intentan herirme me amenazan, trabajando en sus planes engañosos todo el día.
13 Ni kamar kurma ne, wanda ba ya ji, kamar bebe, wanda ba ya iya buɗe bakinsa.
Yo actúo como si fuera sordo con sus palabras, e intento parecer tonto para no tener que hablar.
14 Na zama kamar mutumin da ba ya ji, wanda bakinsa ba ya iya ba da amsa.
Como un hombre que no puede oír, y que no responde, ¡Ese soy yo!
15 Na dogara gare ka, ya Ubangiji; za ka amsa, ya Ubangiji Allahna.
¡Porque espero en ti, Señor! Tú me responderás, Dios mío.
16 Gama na ce, “Kada ka bar su su yi farin ciki a kaina ko su yi kirari a kaina sa’ad da ƙafata ta yi santsi.”
Señor, te pido que por favor mis enemigos no se jacten en frente mí, no dejes que se alegren cuando yo tropiece.
17 Gama ina gab da fāɗuwa, kuma cikin azaba nake kullum.
Porque estoy por colapsar, el dolor nunca se detiene.
18 Na furta laifina; na damu da zunubina.
Confieso mis pecados. Lamento horriblemente todo lo que he hecho.
19 Da yawa ne masu gāba da ni da ƙarfi; waɗanda suke kina ba dalili sun yi yawa.
Tengo enemigos muy poderosos, son bastante activos, y me odian sin razón.
20 Waɗanda suke sāka alherina da mugunta, suna cin zarafina sa’ad da nake bin abin da yake daidai.
Me pagan el bien con mal. Me acusan por el bien que he tratado de hacer.
21 Ya Ubangiji, kada ka yashe ni; kada ka yi nesa da ni, ya Allahna.
Señor, no me abandones, no te alejes de mí.
22 Zo da sauri ka taimake ni, Ya Ubangiji Mai Cetona.
Apresúrate, ven y ayúdame, ¡Oh, Señor, mi salvador!

< Zabura 38 >