< Zabura 34 >
1 Ta Dawuda. Sa’ad da ya yi kamar ya haukace a gaban Abimelek, Wanda ya kore shi, ya kuwa tafi. Zan gode wa Ubangiji kullayaumi; yabonsa kullum za su kasance a leɓunana.
Bendeciré a Yavé en todo tiempo. Su alabanza estará de continuo en mi boca.
2 Raina zai yi fariya a cikin Ubangiji; bari waɗanda suke wahala su ji su kuma yi farin ciki.
En Yavé se gloriará mi alma. Lo oirán los mansos y se alegrarán.
3 Ku ɗaukaka Ubangiji tare da ni; bari mu ɗaukaka sunansa tare.
Engrandezcan a Yavé conmigo, Y exaltemos juntos su Nombre.
4 Na nemi Ubangiji, ya kuwa amsa mini; ya cece ni daga dukan tsoro.
Busqué a Yavé y Él me respondió, Y me libró de todos mis temores.
5 Waɗanda suke dubansa sukan haskaka; fuskokinsu ba sa rufuwa da kunya.
Los que miraron a Él fueron iluminados, Y sus semblantes nunca serán avergonzados.
6 Wannan matalauci ya yi kira, Ubangiji kuwa ya ji shi; ya cece shi daga dukan wahalarsa.
Este pobre clamó, Y Yavé lo escuchó, Y lo salvó de todas sus angustias.
7 Mala’ikan Ubangiji ya kafa sansani kewaye da waɗanda suke tsoronsa, ya kuwa cece su.
El Ángel de Yavé acampa alrededor de los que le temen, Y los rescata.
8 Ku gwada ku gani cewa Ubangiji yana da kyau; mai albarka ne mutumin da yake neman mafaka a gare shi.
Prueben y vean que Yavé es bueno. ¡Cuán feliz es el varón que confía en Él!
9 Ku ji tsoron Ubangiji, ku tsarkakansa, gama masu tsoronsa ba sa rasa kome.
Teman a Yavé, ustedes sus santos, Porque nada falta a los que le temen.
10 Zakoki za su iya rasa ƙarfi su kuma ji yunwa, amma waɗanda suke neman Ubangiji ba sa rasa abu mai kyau.
Los cachorros de león necesitan y sufren hambre, Pero los que buscan a Yavé no carecen de ningún bien.
11 Ku zo,’ya’yana, ku saurare ni; zan koya muku tsoron Ubangiji.
Vengan, hijos, escúchenme. Les enseñaré el temor a Yavé.
12 Duk waninku da yake ƙaunar rayuwa yana kuma so yă ga kwanaki masu kyau,
¿Quién es el hombre que desea vida, Que desea muchos días para ver el bien?
13 ka kiyaye harshenka daga mugunta da kuma leɓunanku daga faɗar ƙarairayi.
Guarda tu boca del mal Y tus labios de hablar engaño.
14 Juyo daga mugunta ku yi alheri; nemi salama ku kuma yi ƙoƙarin samunta.
Apártate del mal y haz el bien. Busca la paz y persíguela.
15 Idanun Ubangiji suna a kan masu adalci kuma kunnuwansa suna sauraran kukansu;
Los ojos de Yavé están hacia los justos, Y sus oídos atentos al clamor de ellos.
16 fuskar Ubangiji yana gāba da waɗanda suke aikata mugunta, don yă sa a manta da su a duniya.
El rostro de Yavé está contra los perversos, Para cortar su memoria de la tierra.
17 Adalai kan yi kuka, Ubangiji kuwa yakan ji su; yakan cece su daga dukan wahalarsu.
Claman los justos, Y Yavé los oye Y los libra de todas sus angustias.
18 Ubangiji yana kusa da waɗanda suka karai ya kuma cece waɗanda aka ragargaza a ruhu.
Cercano está Yavé a los quebrantados de corazón, Y salva a los contritos de espíritu.
19 Adali zai iya kasance da wahala da yawa, amma Ubangiji yakan cece shi daga dukansu;
Muchas son las aflicciones del justo, Pero de todas ellas lo libra Yavé.
20 yakan tsare dukan ƙasusuwansa, ba ko ɗayansu da zai karye.
Él guarda todos sus huesos. Ni uno de ellos es quebrado.
21 Mugunta zai kashe mugu; za a hukunta abokan gāban adalai.
Matará al malo la maldad, Y los que aborrecen al justo serán culpables.
22 Ubangiji yakan cece bayinsa; ba wanda yake neman mafaka a wurinsa da za a hukunta.
Yavé redime la vida de sus esclavos. No serán condenados cuantos en Él confían.