< Zabura 34 >

1 Ta Dawuda. Sa’ad da ya yi kamar ya haukace a gaban Abimelek, Wanda ya kore shi, ya kuwa tafi. Zan gode wa Ubangiji kullayaumi; yabonsa kullum za su kasance a leɓunana.
Ob vseh časih bom blagoslavljal Gospoda, njegova hvala bo nenehno na mojih ustih.
2 Raina zai yi fariya a cikin Ubangiji; bari waɗanda suke wahala su ji su kuma yi farin ciki.
Moja duša bo storila svoje bahanje v Gospodu. Ponižni bodo o tem slišali in bodo veseli.
3 Ku ɗaukaka Ubangiji tare da ni; bari mu ɗaukaka sunansa tare.
Oh poveličujte z menoj Gospoda in skupaj poveličujmo njegovo ime.
4 Na nemi Ubangiji, ya kuwa amsa mini; ya cece ni daga dukan tsoro.
Iskal sem Gospoda in me je uslišal ter me osvobodil pred vsemi mojimi strahovi.
5 Waɗanda suke dubansa sukan haskaka; fuskokinsu ba sa rufuwa da kunya.
Pogledali so k njemu in bili ožarjeni in njihovi obrazi niso bili osramočeni.
6 Wannan matalauci ya yi kira, Ubangiji kuwa ya ji shi; ya cece shi daga dukan wahalarsa.
Ta revež je zajokal in Gospod ga je uslišal ter ga rešil pred vsemi njegovimi težavami.
7 Mala’ikan Ubangiji ya kafa sansani kewaye da waɗanda suke tsoronsa, ya kuwa cece su.
Gospodov angel tabori okoli teh, ki se ga bojijo in jih osvobaja.
8 Ku gwada ku gani cewa Ubangiji yana da kyau; mai albarka ne mutumin da yake neman mafaka a gare shi.
Oh okusite in vidite, da je Gospod dober. Blagoslovljen je človek, ki zaupa vanj.
9 Ku ji tsoron Ubangiji, ku tsarkakansa, gama masu tsoronsa ba sa rasa kome.
Oh bojte se Gospoda, vi njegovi sveti, kajti nič ne manjka tem, ki se ga bojijo.
10 Zakoki za su iya rasa ƙarfi su kuma ji yunwa, amma waɗanda suke neman Ubangiji ba sa rasa abu mai kyau.
Mladim levom primanjkuje in trpijo lakoto, toda tistim, ki iščejo Gospoda, ne bo manjkala nobena dobra stvar.
11 Ku zo,’ya’yana, ku saurare ni; zan koya muku tsoron Ubangiji.
Pridite, otroci, prisluhnite mi. Strahu Gospodovega vas bom učil.
12 Duk waninku da yake ƙaunar rayuwa yana kuma so yă ga kwanaki masu kyau,
Kakšen človek je tisti, ki želi življenje in ljubi mnoge dneve, da bi lahko videl dobro?
13 ka kiyaye harshenka daga mugunta da kuma leɓunanku daga faɗar ƙarairayi.
Zadržuj svoj jezik pred zlom in svoje ustnice od govorjenja zvijače.
14 Juyo daga mugunta ku yi alheri; nemi salama ku kuma yi ƙoƙarin samunta.
Odidi od zla in delaj dobro, išči mir in ga zasleduj.
15 Idanun Ubangiji suna a kan masu adalci kuma kunnuwansa suna sauraran kukansu;
Gospodove oči so na pravičnih in njegova ušesa so odprta k njihovemu klicanju.
16 fuskar Ubangiji yana gāba da waɗanda suke aikata mugunta, don yă sa a manta da su a duniya.
Gospodovo obličje je zoper te, ki delajo zlo, da z zemlje iztrebi spomin na njih.
17 Adalai kan yi kuka, Ubangiji kuwa yakan ji su; yakan cece su daga dukan wahalarsu.
Pravični kličejo in Gospod uslišuje ter jih osvobaja iz vseh njihovih stisk.
18 Ubangiji yana kusa da waɗanda suka karai ya kuma cece waɗanda aka ragargaza a ruhu.
Gospod je blizu tem, ki so zlomljenega srca in rešuje takšne, ki so skesanega duha.
19 Adali zai iya kasance da wahala da yawa, amma Ubangiji yakan cece shi daga dukansu;
Mnoge so stiske pravičnega, toda Gospod ga osvobaja iz njih vseh.
20 yakan tsare dukan ƙasusuwansa, ba ko ɗayansu da zai karye.
Varuje vse njegove kosti niti ena izmed njih ni zlomljena.
21 Mugunta zai kashe mugu; za a hukunta abokan gāban adalai.
Zlo bo pokončalo zlobnega in tisti, ki sovražijo pravične, bodo zapuščeni.
22 Ubangiji yakan cece bayinsa; ba wanda yake neman mafaka a wurinsa da za a hukunta.
Gospod odkupuje dušo svojih služabnikov in nobeden od teh, ki zaupajo vanj, ne bo zapuščen.

< Zabura 34 >