< Zabura 25 >

1 Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
A ti, oh SEÑOR, mi alma enaltece.
2 A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
Oh Dios mío, he puesto mi fe en ti, no me avergüences; no permitas que mis enemigos se glorien sobre mí.
3 Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
No se avergüence ningún siervo tuyo que en ti confía; serán avergonzados aquellos que se rebelan sin causa.
4 Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
Muéstrame tus caminos, oh Señor; enséñame tus senderos.
5 ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
Sé mi guía y maestro de la manera verdadera; porque tú eres el Dios de mi salvación; Estoy esperando tu palabra todo el día.
6 Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
Oh Señor, ten en cuenta tu compasión y tus misericordias; que son perpetuas.
7 Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
No tengas en cuenta mis pecados cuando era joven, o mi maldad: deja que tu recuerdo de mí esté lleno de misericordia, oh Señor, por tu gran amor y bondad.
8 Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
Bueno y justo es el Señor: entonces él enseñará a los pecadores el camino.
9 Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
Y guía para los pobres en espíritu: enseñará a los mansos el camino.
10 Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
Todos los caminos del Señor son misericordia y verdad para aquellos que mantienen su pacto y su testimonio.
11 Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
Por tu nombre, oh Señor, permíteme tener perdón por mi pecado, que es muy grande.
12 To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
Si un hombre tiene temor del Señor, el Señor le enseñará el camino que debe seguir,
13 Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
gozará de bienestar, y su simiente tendrá la tierra por su herencia.
14 Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
La comunión íntima de Jehová es con los que le temen, con aquellos en cuyo corazón está el temor de él; y a ellos hará conocer su pacto.
15 Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
Mis ojos se vuelven al Señor todo el tiempo; porque él sacará mis pies de la red.
16 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
Mírame Señor ten misericordia de mí; porque estoy solo y preocupado.
17 Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
Los problemas de mi corazón aumentan: Oh sácame de mis dolores.
18 Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
Mira mi penas y mi dolor; y perdona todos mis pecados.
19 Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
Mira cómo aumentan los que están en mi contra, con su odio violento me aborrecen.
20 Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
Guarda mi alma, y ​​arráncame fuera de peligro; no me avergüences, porque he puesto mi fe en ti.
21 Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
Que mis caminos limpios y rectos me protejan, porque mi esperanza está en ti.
22 Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!
Dale a Israel salvación, oh Dios, de todas sus angustias.

< Zabura 25 >