< Zabura 25 >
1 Ta Dawuda. A gare ka Ya Ubangiji, na miƙa raina.
A Psalme of David. Unto thee, O Lord, lift I vp my soule.
2 A gare ka na dogara, ya Allahna. Kada ka bari in sha kunya, ko ka bar abokan gābana su yi nasara a kaina.
My God, I trust in thee: let me not be confounded: let not mine enemies reioyce ouer mee.
3 Ba wanda yake sa bege a gare ka da zai taɓa shan kunya, amma za su sha kunya su da suke tayarwa babu dalili.
So all that hope in thee, shall not be ashamed: but let them be confounded, that transgresse without cause.
4 Ka nuna mini hanyoyinka, ya Ubangiji, ka koya mini hanyoyinka;
Shew me thy waies, O Lord, and teache me thy paths.
5 ka bi da ni cikin gaskiyarka ka kuma koya mini, gama kai ne Allah Mai cetona, kuma begena yana a kanka dukan yini.
Leade me foorth in thy trueth, and teache me: for thou art the God of my saluation: in thee doe I trust all the day.
6 Ka tuna, ya Ubangiji da jinƙai da kuma ƙaunarka mai girma, gama suna nan tun dā.
Remember, O Lord, thy tender mercies, and thy louing kindnesse: for they haue beene for euer.
7 Kada ka tuna da zunuban ƙuruciyata da kuma hanyoyin tawayena; bisa ga ƙaunarka ka tuna da ni, gama kai nagari ne, ya Ubangiji.
Remember not the sinnes of my youth, nor my rebellions, but according to thy kindenesse remember thou me, euen for thy goodnesse sake, O Lord.
8 Ubangiji nagari da mai adalci ne; saboda haka yakan koyar da masu zunubi a hanyoyinsa.
Gracious and righteous is the Lord: therefore will he teache sinners in the way.
9 Yakan bi da masu tawali’u cikin abin da yake daidai ya kuma koyar da su hanyoyinsa.
Them that be meeke, will hee guide in iudgement, and teach the humble his way.
10 Dukan hanyoyin Ubangiji ƙaunatattu ne da kuma aminci ga waɗanda suke kiyaye abin da alkawari ya bukaci.
All the pathes of the Lord are mercie and trueth vnto such as keepe his couenant and his testimonies.
11 Saboda sunanka, ya Ubangiji, ka gafarta laifina, ko da yake mai girma ne.
For thy Names sake, O Lord, be merciful vnto mine iniquitie, for it is great.
12 To wane ne mai tsoron Ubangiji? Zai koyar da shi a hanyar da ya zaɓa masa.
What man is he that feareth the Lord? him wil he teache the way that hee shall chuse.
13 Zai ci kwanakinsa a wadace, kuma zuriyarsa za su gāji ƙasar.
His soule shall dwell at ease, and his seede shall inherite the land.
14 Ubangiji yakan amince da waɗanda suke tsoronsa; yakan sa su san alkawarinsa.
The secrete of the Lord is reueiled to them, that feare him: and his couenant to giue them vnderstanding.
15 Idanuna kullum suna a kan Ubangiji, gama shi ne kaɗai zai kuɓutar da ƙafafuna daga tarko.
Mine eyes are euer towarde the Lord: for he will bring my feete out of the net.
16 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, gama na kaɗaice ina kuma wahala.
Turne thy face vnto mee, and haue mercie vpon me: for I am desolate and poore.
17 Damuwoyin zuciyata sun ninka; ka’yantar da ni daga wahalata.
The sorowes of mine heart are enlarged: drawe me out of my troubles.
18 Ka dubi wahalata da kuma azabata ka ɗauke mini dukan zunubaina.
Looke vpon mine affliction and my trauel, and forgiue all my sinnes.
19 Dubi yadda abokan gābana sun ƙaru da kuma yadda suka ƙara ƙina!
Beholde mine enemies, for they are manie, and they hate me with cruell hatred.
20 Ka tsare raina ka kuma kuɓutar da ni; kada ka bari in sha kunya, gama na nemi mafaka daga gare ka.
Keepe my soule, and deliuer me: let me not be confounded, for I trust in thee.
21 Bari mutunci da adalci su tsare ni, domin begena yana a kanka.
Let mine vprightnes and equitie preserue me: for mine hope is in thee.
22 Ka fanshi Isra’ila, ya Allah, daga dukan wahalarsu!
Deliuer Israel, O God, out of all his troubles.