< Zabura 23 >

1 Zabura ta Dawuda. Ubangiji ne yake kiwona, ba zan rasa kome ba,
O Senhor é o meu pastor, nada me faltará.
2 Yakan sa in kwanta a makiyaya mai ɗanyar ciyawa, yakan bi da ni kusa da ruwaye marar hayaniya,
Deitar-me faz em verdes pastos, guia-me mansamente a aguas mui quietas.
3 yakan maido da raina. Yakan bi da ni a hanyoyin adalci saboda sunansa.
Refrigera a minha alma; guia-me pelas veredas da justiça, por amor do seu nome.
4 Ko da na yi tafiya ta kwari na inuwar mutuwa, ba zan ji tsoron mugu ba, gama kana tare da ni; bulalarka na dūka da kuma sandanka na tafiya, za su yi mini ta’aziyya.
Ainda que eu andasse pelo valle da sombra da morte, não temeria mal algum, porque tu estás comigo; a tua vara e o teu cajado me consolam.
5 Ka shirya mini tebur a gaban abokan gābana. Ka shafe kaina da mai; kwaf nawa ya cika har yana zuba.
Preparas uma mesa perante mim na presença dos meus inimigos, unges a minha cabeça com oleo, o meu calix trasborda.
6 Tabbatacce alheri da ƙauna za su bi dukan kwanakin raina, zan kuwa zauna a gidan Ubangiji har abada.
Certamente que a bondade e a misericordia me seguirão todos os dias da minha vida: e habitarei na casa do Senhor por longos dias.

< Zabura 23 >