< Zabura 23 >

1 Zabura ta Dawuda. Ubangiji ne yake kiwona, ba zan rasa kome ba,
Cantique de David. L’Éternel est mon berger: je ne manquerai de rien.
2 Yakan sa in kwanta a makiyaya mai ɗanyar ciyawa, yakan bi da ni kusa da ruwaye marar hayaniya,
Il me fait reposer dans de verts pâturages, Il me dirige près des eaux paisibles.
3 yakan maido da raina. Yakan bi da ni a hanyoyin adalci saboda sunansa.
Il restaure mon âme, Il me conduit dans les sentiers de la justice, A cause de son nom.
4 Ko da na yi tafiya ta kwari na inuwar mutuwa, ba zan ji tsoron mugu ba, gama kana tare da ni; bulalarka na dūka da kuma sandanka na tafiya, za su yi mini ta’aziyya.
Quand je marche dans la vallée de l’ombre de la mort, Je ne crains aucun mal, car tu es avec moi: Ta houlette et ton bâton me rassurent.
5 Ka shirya mini tebur a gaban abokan gābana. Ka shafe kaina da mai; kwaf nawa ya cika har yana zuba.
Tu dresses devant moi une table, En face de mes adversaires; Tu oins d’huile ma tête, Et ma coupe déborde.
6 Tabbatacce alheri da ƙauna za su bi dukan kwanakin raina, zan kuwa zauna a gidan Ubangiji har abada.
Oui, le bonheur et la grâce m’accompagneront Tous les jours de ma vie, Et j’habiterai dans la maison de l’Éternel Jusqu’à la fin de mes jours.

< Zabura 23 >