< Zabura 22 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da salon “Matar Zomon Safiya.” Zabura ta Dawuda. Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni? Me ya sa ka yi nisa da cetona, ka yi nesa daga kalmomin nishina?
Jusqu'à la Fin, pour la prière du matin, psaume de David. Ô Dieu, ô mon Dieu, regarde-moi; pourquoi m'as-tu délaissé? la voix de mes péchés a fait fuir mon salut.
2 Ya Allahna, na yi kuka da rana, amma ba ka amsa ba, da dare kuma ban yi shiru ba.
Ô mon Dieu, je crierai vers toi le jour, et tu ne m'exauceras point; je crierai la nuit, et ce n'est point folie à moi.
3 Duk da haka kana a kursiyi a matsayin Mai Tsarkin nan; kai ne yabon Isra’ila.
Mais toi, gloire d'Israël, tu résides au lieu saint.
4 A gare ka ne kakanninmu suka sa bege; sun dogara ka kuwa cece su.
Nos pères ont espéré en toi; ils ont espéré, et tu les as délivrés.
5 Sun yi kuka gare ka suka kuma sami ceto; a gare ka suka dogara kuma ba su sha kunya ba.
Ils ont crié vers toi, et ils ont été sauvés; ils ont espéré en toi, et n'ont point été confondus.
6 Amma ni dai tsutsa ne ba mutum ba, wanda mutane suke yi wa ba’a suka kuma rena shi.
Mais moi je suis un ver de terre et non un homme; opprobre des hommes et mépris du peuple.
7 Duk wanda ya gan ni yakan yi mini ba’a; suna yin mini ashar, suna kaɗa kansu suna cewa,
Tous ceux qui m'ont vu se sont moqués de moi; ils ont murmuré entre leurs lèvres, ils ont secoué la tête.
8 “Ya dogara ga Ubangiji; bari Ubangiji yă cece shi. Bari yă cece shi, da yake yana jin daɗinsa.”
(Ils ont dit): Il a mis son espoir en Dieu, que le Seigneur le sauve; qu'il le délivre, puisqu'il se complaît en lui.
9 Duk da haka ka fitar da ni daga ciki; ka sa na dogara gare ka, ko ma a ƙirjin mahaifiyata.
C'est toi, il est vrai, qui m'as tiré des entrailles de ma mère; et, à sa mamelle, j'espérais en toi.
10 Daga haihuwa an jefa ni a kanka; daga cikin mahaifiyata kai ne Allahna.
Aussitôt sorti de son sein, j'ai été livré à toi; tu es mon Dieu dès le sein de ma mère.
11 Kada ka yi nesa da ni, gama wahala na kusa kuma babu wani da zai taimaka.
Ne t'éloigne point de moi; car l'affliction est proche, et nul ne me porte secours.
12 Bijimai masu yawa sun kewaye ni; bijimai masu ƙarfi na Bashan sun sa ni a tsaka.
Une multitude de jeunes taureaux m'investissent, des bœufs robustes m'ont entouré,
13 Zakoki masu ruri suna yayyage abin da suka kama sun buɗe bakunansu a kaina.
Et ont ouvert contre moi leur bouche, comme un lion ravisseur et rugissant.
14 An zubar da ni kamar ruwa, kuma dukan ƙasusuwana sun fiffito daga mahaɗai. Zuciyata ta zama kaki; ta narke a cikina.
Je me suis répandu comme de l'eau; tous mes os ont été dispersés; mon cœur dans ma poitrine est devenu comme de la cire liquide.
15 Ƙarfina ya bushe kamar kasko, harshena kuma ya manne wa dasashina na sama; ka kwantar da ni a ƙurar mutuwa.
Ma force s'est desséchée comme la brique; ma langue s'est collée à mon palais, et tu m'as poussé dans la poussière de la mort.
16 Karnuka sun kewaye ni; ƙungiyar mugaye sun sa ni a tsaka, sun soki hannuwana da ƙafafuna.
Une multitude de chiens m'ont entouré; la synagogue des pervers m'assiège; ils m'ont percé les pieds et les mains,
17 Zan iya ƙirga ƙasusuwana; mutane suna farin ciki a kaina.
Ils ont compté mes os; ils m'ont observé et surveillé.
18 Sun raba rigunana a tsakaninsu suka kuma jefa ƙuri’a a kan rigunana.
Ils se sont partagé mes vêtements, et ils ont tiré ma robe au sort.
19 Amma kai, ya Ubangiji, kada ka yi nisa; Ya Ƙarfina zo da sauri don ka taimake ni.
Et toi, ô Seigneur, n'éloigne pas de moi ton secours, songe à ma défense.
20 Ka ceci raina daga takobi, raina mai daraja daga ikon karnuka.
Délivre mon âme du glaive; délivre de la griffe des chiens mon unique.
21 Ka cece ni daga bakin zakoki; ka cece ni daga ƙahonin ɓauna.
Tire-moi de la gueule du lion, et sauve ma faiblesse de la corne des licornes.
22 Zan furta sunanka ga’yan’uwana; cikin taron masu sujada zan yabe ka.
Je célébrerai ton nom parmi mes frères; Je te chanterai au milieu de l'église.
23 Ku da kuke tsoron Ubangiji, ku yabe shi! Dukanku zuriyar Yaƙub, ku girmama shi! Ku girmama shi, dukanku zuriyar Isra’ila!
Ô vous qui craignez le Seigneur, louez-le; et toi, peuple de Jacob, glorifie-le. Que toute la race d'Israël le craigne,
24 Gama bai rena ko yă ƙyale wahalar masu shan wuya ba; bai ɓoye fuskarsa daga gare shi ba amma ya saurari kukansa na neman taimako.
Parce qu'il n'a ni méprisé ni rebuté la prière des pauvres; parce qu'il n'a point détourné de moi son visage; parce qu'il m'a exaucé quand j'ai crié vers lui.
25 Daga gare ka yabona yake zuwa cikin babban taro; a gaban waɗanda suke tsoronka zan cika alkawarina.
Tu seras ma louange dans la grande église; j'accomplirai mes vœux devant tous ceux qui te craignent.
26 Matalauta za su ci su ƙoshi; su da suke neman Ubangiji za su yabe shi, bari zukatanku su rayu har abada!
Les pauvres mangeront, et ils seront rassasiés; et ceux qui cherchent le Seigneur le loueront; leurs cœurs vivront dans tous les siècles des siècles.
27 Dukan iyakokin duniya za su tuna su kuma juya ga Ubangiji, kuma dukan iyalan al’ummai za su rusuna a gabansa,
Et jusqu'aux confins de la terre on se souviendra du Seigneur; on se convertira à lui; toutes les tribus des Gentils se prosterneront devant lui pour l'adorer.
28 gama mulki na Ubangiji ne kuma yana mulki a bisa al’ummai.
Car la royauté appartient au Seigneur; il régnera sur les nations.
29 Dukan attajiran duniya za su yi biki su kuma yi sujada; dukan waɗanda suka gangara zuwa ƙura za su durƙusa a gabansa, waɗanda ba za su iya bar kansu da rai ba.
Tous les riches de la terre ont mangé et adoré; tous ceux qui descendent en la terre tomberont devant lui. Que mon âme aussi vive pour lui,
30 Zuriya masu zuwa za su yi masa hidima; za a faɗa wa zuriya na nan gaba game da Ubangiji.
Toute ma postérité le servira. La génération future sera annoncée au Seigneur;
31 Za su yi shelar adalcinsa ga mutanen da ba a riga an haifa ba, gama ya aikata shi.
On fera connaître sa justice au peuple qui doit naître, et que le Seigneur s'est préparé.

< Zabura 22 >