< Zabura 20 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ubangiji ya amsa maka sa’ad da ka yi kira cikin wahala; bari sunan Allah na Yaƙub yă kiyaye ka.
За първия певец. Давидов псалом. Господ да те послуша в скръбен ден; Името на Бога Яковов да те постави на високо!
2 Bari yă aiko maka da taimako daga wuri mai tsarki yă kuma ba ka gudummawa daga Sihiyona.
Да ти прати помощ от светилището, И да те подкрепи от Сион!
3 Bari yă tuna da dukan sadakokinka yă kuma karɓi hadayunka na ƙonawa. (Sela)
Да си спомни всичките твои приноси, И да приеме всеизгарянето ти! (Села)
4 Bari yă biya maka bukatan ranka yă kuma sa dukan shirye-shiryenka su yi nasara.
Да ти даде според желанието на сърцето ти, И да изпълни всяко твое намерение!
5 Za mu yi sowa ta farin ciki sa’ad da ka yi nasara mu kuma ɗaga tutotinmu a cikin sunan Allahnmu. Bari Ubangiji yă biya maka dukan bukatunka.
В спасението Ти ще се зарадваме, И в името на нашия Бог ще издигнем знамена. Господ да изпълни всичките твои прошения!
6 Yanzu na san cewa, Ubangiji yakan cece shafaffensa. Yakan amsa masa daga samansa mai tsarki da ikon ceto na hannun damansa.
Сега зная, че Господ избави помазаника Си; Що го слуша от своето Си небе Със спасителна сила на десницата Си.
7 Waɗansu sun dogara a kekunan yaƙi waɗansu kuma a dawakai, amma mu, mun dogara a cikin sunan Ubangiji Allahnmu.
Едни споменават колесници, а други коне; Но ние ще споменем името на Господа нашия Бог.
8 Za a durƙusar da su, su kuma fāɗi, amma mu za mu tashi mu tsaya daram.
Те се спънаха и паднаха; А ние станахме и се изправихме.
9 Ya Ubangiji, ka ba da nasara ga sarki! Ka amsa mana sa’ad da muka yi kira!
Господи пази! Нека ни послуша Царят, когато Го призовем.