< Zabura 18 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
Müzik şefi için - RAB'bin kulu Davut'un mezmuru - RAB kendisini bütün düşmanlarının pençesinden ve Saul'un elinden kurtardığı gün Davut RAB'be şu ezgiyi okudu: Seni seviyorum, gücüm sensin, ya RAB!
2 Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
RAB benim kayam, sığınağım, kurtarıcımdır, Tanrım, kayam, sığınacak yerimdir, Kalkanım, güçlü kurtarıcım, korunağımdır!
3 Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
Övgüye değer RAB'be seslenir, Kurtulurum düşmanlarımdan.
4 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
Ölüm iplerine dolanmıştım, Yıkım selleri basmıştı beni,
5 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol )
Ölüler diyarının bağları sarmıştı, Ölüm tuzakları çıkmıştı karşıma. (Sheol )
6 Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
Sıkıntı içinde RAB'be yakardım, Yardıma çağırdım Tanrım'ı. Tapınağından sesimi duydu, Haykırışım kulaklarına ulaştı.
7 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
O zaman yeryüzü sarsılıp sallandı, Titreyip sarsıldı dağların temelleri, Çünkü RAB öfkelenmişti.
8 Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
Burnundan duman yükseldi, Ağzından kavurucu ateş Ve korlar fışkırdı.
9 Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
Kara buluta basarak Gökleri yarıp indi.
10 Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
Bir Keruv'a binip uçtu, Rüzgar kanatlar takarak hızla geldi.
11 Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
Karanlığı örtündü, Kara bulutları kendine çardak yaptı.
12 daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
Varlığının parıltısından, Bulutlardan dolu ve korlar savruluyordu.
13 Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
RAB göklerden gürledi, Duyurdu sesini Yüceler Yücesi, Dolu ve alevli korlarla.
14 Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
Savurup oklarını düşmanlarını dağıttı, Şimşek çaktırarak onları şaşkına çevirdi.
15 Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
Denizin dibi göründü, Yeryüzünün temelleri açığa çıktı, ya RAB, Senin azarlamandan, Burnundan çıkan güçlü soluktan.
16 Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
RAB yukarıdan elini uzatıp tuttu, Çıkardı beni derin sulardan.
17 Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
Beni zorlu düşmanımdan, Benden nefret edenlerden kurtardı, Çünkü onlar benden güçlüydü.
18 Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
Felaket günümde karşıma dikildiler, Ama RAB bana destek oldu.
19 Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
Beni huzura kavuşturdu, Kurtardı, çünkü benden hoşnut kaldı.
20 Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
RAB doğruluğumun karşılığını verdi, Beni temiz ellerime göre ödüllendirdi.
21 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
Çünkü RAB'bin yolunda yürüdüm, Tanrım'dan uzaklaşarak kötülük yapmadım.
22 Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
O'nun bütün ilkelerini göz önünde tuttum, Kurallarından ayrılmadım.
23 Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
O'nun gözünde kusursuzdum, Suç işlemekten sakındım.
24 Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
Bu yüzden RAB beni doğruluğuma Ve gözünde pak olan ellerime göre ödüllendirdi.
25 Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
Sadık kuluna sadakat gösterir, Kusursuz olana kusursuz davranırsın.
26 ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
Pak olanla pak olur, Eğriye eğri davranırsın.
27 Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
Alçakgönüllüleri kurtarır, Gururluların başını eğersin.
28 Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
Işığımın kaynağı sensin, ya RAB, Tanrım! Karanlığımı aydınlatırsın.
29 Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
Desteğinle akıncılara saldırır, Seninle surları aşarım, Tanrım.
30 Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
Tanrı'nın yolu kusursuzdur, RAB'bin sözü arıdır. O kendisine sığınan herkesin kalkanıdır.
31 Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
Var mı RAB'den başka tanrı? Tanrımız'dan başka kaya var mı?
32 Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
Tanrı beni güçle donatır, Yolumu kusursuz kılar.
33 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
Ayaklar verdi bana, geyiklerinki gibi, Doruklarda tutar beni.
34 Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
Bana savaşmayı öğretti, Kollarımla tunç bir yayı gereyim diye.
35 Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
Bana zafer kalkanını bağışlarsın, Sağ elin destekler, Alçakgönüllülüğün yüceltir beni.
36 Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
Bastığım yerleri genişletirsin, Burkulmaz bileklerim.
37 Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
Kovalayıp yetiştim düşmanlarıma, Hepsi yok olmadan geri dönmedim.
38 Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
Ezdim onları, kalkamaz oldular, Ayaklarımın altına serildiler.
39 Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
Savaş için beni güçle donattın, Bana başkaldıranları önümde yere serdin.
40 Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
Düşmanlarımı kaçmak zorunda bıraktın, Benden nefret edenleri yok ettim.
41 Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
Feryat ettiler, ama kurtaran çıkmadı; RAB'bi çağırdılar, ama O yanıt vermedi.
42 Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
Ezdim onları, rüzgarın savurduğu toza döndüler, Sokak çamuru gibi savurup attım.
43 Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
Halkımın çekişmelerinden beni kurtardın, Ulusların önderi yaptın, Tanımadığım halklar bana kulluk ediyor.
44 da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
Duyar duymaz sözümü dinlediler, Yabancılar bana yaltaklandılar.
45 Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
Yabancıların betleri benizleri attı, Titreyerek çıktılar kalelerinden.
46 Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
RAB yaşıyor! Kayam'a övgüler olsun! Yücelsin kurtarıcım Tanrı!
47 Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
O'dur öcümü alan, Halkları bana bağımlı kılan.
48 wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
Düşmanlarımdan kurtarır, Başkaldıranlardan üstün kılar beni, Zorbaların elinden alır.
49 Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
Bunun için uluslar arasında sana şükredeceğim, ya RAB, Adını ilahilerle öveceğim.
50 Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.
RAB kralını büyük zaferlere ulaştırır, Meshettiği krala, Davut'a ve soyuna Sonsuza dek sevgi gösterir.