< Zabura 18 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda bawan Ubangiji. Ya rera ta ga Ubangiji kalmomin wannan waƙa sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa da kuma daga hannun Shawulu, ya ce, Ina ƙaunarka, ya Ubangiji, ƙarfina.
Amarte he, Jehová, fortaleza mía.
2 Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona; Allahna shi ne dutsena, a gare shi nake neman mafaka. Shi ne garkuwata da ƙahon cetona, mafakata.
Jehová, roca mía, y castillo mío, y escapador mío; Dios mío, fuerte mío: confiarme he en él: escudo mío, y el cuerno de mi salud; refugio mío.
3 Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa kuɓuta daga abokan gābana.
Al alabado Jehová invocaré, y seré salvo de mis enemigos.
4 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni; rigyawan hallaka sun sha kaina.
Cercáronme dolores de muerte, y arroyos de perversidad me atemorizaron:
5 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe kewaye da ni; tarkon mutuwa ya yi mini arangama. (Sheol )
Dolores del sepulcro me rodearon; anticipáronme lazos de muerte: (Sheol )
6 Cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; Na yi kuka ga Allahna don taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa.
En mi angustia llamé a Jehová, y clamé a mi Dios: él oyó desde su templo mi voz, y mi clamor entró delante de él, en sus orejas.
7 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, tussan duwatsu sun girgiza; sun yi rawa domin ya yi fushi.
Y la tierra fue conmovida y tembló: y los fundamentos de los montes se estremecieron, y se removieron, porque él se enojó.
8 Hayaƙi ya tashi daga kafan hancinsa; wuta mai ci daga bakinsa, garwashi wuta mai ci daga bakinsa.
Subió humo en su nariz, y de su boca fuego quemante: carbones se encendieron de él.
9 Ya buɗe sammai ya sauko; baƙaƙen gizagizai suna a ƙarƙashin ƙafafunsa.
Y abajó los cielos, y descendió; y oscuridad debajo de sus pies.
10 Ya hau kerubobi ya kuma yi firiya; ya yi shawagi a fikafikan iska.
Y cabalgó sobre un querubín, y voló: y voló sobre las alas del viento.
11 Ya mai da duhu abin rufuwarsa, rumfa kewaye da shi, baƙaƙen gizagizan ruwan sama na sarari,
Puso tinieblas por su escondedero: en sus en derredores de su tabernáculo, oscuridad de aguas, nubes de los cielos.
12 daga cikin hasken kasancewarsa gizagizai suka yi gaba, da ƙanƙara da kuma walƙiya.
Por el resplandor de delante de él sus nubes pasaron: granizo y carbones de fuego.
13 Ubangiji ya yi tsawa daga sama; muryar Mafi Ɗaukaka ya yi kāra.
Y tronó en los cielos Jehová, y el Altísimo dio su voz: granizo y carbones de fuego.
14 Ya harba kibiyoyinsa ya kuma watsar da abokan gāba, walƙiya mai girma ya fafare su.
Y envió sus saetas y desbaratólos: y echó relámpagos, y los destruyó.
15 Kwarin teku sun bayyana tussan duniya sun bayyana a fili sa’ad da ka tsawata, ya Ubangiji, sa’ad da ka numfasa daga hancinka.
Y aparecieron las honduras de las aguas: y descubriéronse los cimientos del mundo por tu reprensión, o! Jehová, por el soplo del viento de tu nariz.
16 Ya miƙa hannunsa daga sama ya kama ni; ya ja ni daga zurfin ruwaye.
Envió desde lo alto, me tomó, me sacó de las muchas aguas.
17 Ya cece ni daga abokin gābana mai ƙarfi, daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina.
Me escapó de mi fuerte enemigo, y de los que me aborrecieron: aunque ellos eran más fuertes que yo.
18 Sun yi arangama da ni a ranar masifa, amma Ubangiji ya zama mai taimakona.
Anticipáronme en el día de mi quebrantamiento: mas Jehová me fue por bordón.
19 Ya fitar da ni zuwa wuri mai sarari; ya kuɓutar da ni, gama yana jin daɗina.
Y me sacó a anchura: me libró, porque se agradó de mí.
20 Ubangiji ya yi haka da ni bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya ba ni lada.
Jehová me pagará conforme a mi justicia: conforme a la limpieza de mis manos me volverá.
21 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi mugunta ta wurin juyewa daga Allahna ba.
Por cuanto guardé los caminos de Jehová: y no me maleé con mi Dios.
22 Dukan dokokinsa suna a gābana; ban juye daga ƙa’idodinsa ba.
Porque todos sus juicios estuvieron delante de mí: y no eché de mí sus estatutos.
23 Na kasance marar laifi a gabansa na kuma kiyaye kaina daga zunubi.
Y fui perfecto con él: y me recaté de mi maldad.
24 Ubangiji ya ba ni lada bisa ga adalcina, bisa ga tsabtan hannuwana a gabansa.
Y pagóme Jehová conforme a mi justicia: conforme a la limpieza de mis manos delante de sus ojos.
25 Ga mai aminci ka nuna kanka mai aminci, ga marar laifi ka nuna kanka marar laifi,
Con el misericordioso serás misericordioso: y con el varón perfecto serás perfecto.
26 ga mai tsabta ka nuna kanka mai tsabta, amma ga karkatacce, ka nuna kanka mai wayo.
Con el limpio serás limpio, y con el perverso serás perverso.
27 Kakan cece mai sauƙinkai amma kakan ƙasƙantar da masu girman kai.
Por tanto tú al pueblo humilde salvarás: y los ojos altivos humillarás.
28 Kai Ya Ubangiji, ka sa fitilata ta yi ta ci; Allahna ya mai da duhu ya zama haske.
Por tanto tú alumbrarás mi candela: Jehová, mi Dios, alumbrará mis tinieblas,
29 Da taimakonka zan iya fāɗa wa runduna; tare da Allahna zan iya rinjayi katanga.
Porque contigo desharé ejércitos: y en mi Dios asaltaré muros.
30 Game da Allah kuwa, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji marar kuskure ne. Shi garkuwa ne ga dukan waɗanda suke neman mafaka a gare shi.
Dios, perfecto su camino: la palabra de Jehová afinada: escudo es a todos los que esperan en él.
31 Gama wane ne Allah in ba Ubangiji ba? Wane ne kuwa Dutse in ba Allahnmu ba?
Porque ¿qué Dios hay fuera de Jehová? ¿y qué fuerte fuera de nuestro Dios?
32 Allah ne ya ƙarfafa ni da ƙarfi ya kuma sa hanyarta ta zama cikakkiya.
Dios, que me ciñe de fuerza; e hizo perfecto mi camino:
33 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsaya a kan ƙwanƙoli.
Que pone mis pies como pies de ciervas: y me hizo estar sobre mis alturas:
34 Ya horar da hannuwana don yaƙi; hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
Que enseña mis manos para la batalla; y el arco de acero será quebrado con mis brazos.
35 Ka ba ni garkuwar nasara, kuma hannunka na dama yana riƙe ni; ya sunkuya don ka mai da ni mai girma.
Y me diste el escudo de tu salud; y tu diestra me sustentará, y tu mansedumbre me multiplicará.
36 Ka fadada hanyar da yake a ƙarƙashina, don kada ɗiɗɗigena yă juya.
Ensancharás mi paso debajo de mí, y no titubearán mis rodillas.
37 Na bi abokan gābana na kuma cim musu; ban juya ba sai da na hallaka su.
Perseguiré mis enemigos, y alcanzarles he; y no volveré hasta acabarles.
38 Na ragargaza su har ba za su iya tashi ba; sun fāɗi a ƙarƙashin ƙafafuna.
Herírles he, y no podrán levantarse: caerán debajo de mis pies.
39 Ka ƙarfafa ni da ƙarfi saboda yaƙi; ka sa abokan gābana suka rusuna mini.
Y ceñísteme de fortaleza para la pelea: agobiaste mis enemigos debajo de mí.
40 Ka sa abokan gābana suka juya suka gudu, na kuma hallaka abokan gābana.
Y dísteme la cerviz de mis enemigos: y a los que me aborrecían, destruí.
41 Sun nemi taimako, amma ba su sami wanda zai cece su ba, ga Ubangiji, amma bai amsa ba.
Clamaron, y no hubo quien salvase: a Jehová, mas no les oyó.
42 Na murƙushe su kamar ƙura mai laushi da iska ke kwashewa; na zubar da su kamar laka a tituna.
Y los molí como polvo delante del viento: como a lodo de las calles los esparcí.
43 Ka cece ni daga harin mutane; ka mai da ni kan al’ummai. Mutanen da ban sani ba sun zama bayina,
Librásteme de contiendas de pueblo: pusísteme por cabecera de gentes; pueblo que no conocí, me sirvió.
44 da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya; baƙi suna rusuna a gabana.
A oída de oreja me obedeció: los hombres extraños me mintieron.
45 Duk sukan karai; suna zuwa da rawan jiki daga mafakansu.
Los hombres extraños se cayeron: y tuvieron miedo desde sus encerramientos.
46 Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga Dutsena! Girma ya tabbata ga Allah Mai cetona!
Viva Jehová, y bendito sea mi fuerte: y sea ensalzado el Dios de mi salud.
47 Shi ne Allah mai sāka mini, wanda yake sa al’ummai a ƙarƙashina,
El Dios que me da las venganzas, y sujetó pueblos debajo de mí.
48 wanda yakan cece ni daga abokan gābana. Ana girmama ka bisa abokan gābana; daga masu tā-da-na-zaune-tsaye ka kuɓutar da ni.
Mi librador de mis enemigos: también me hiciste superior de mis adversarios: de varón violento me libraste.
49 Saboda haka zan yabe ka a cikin al’ummai, ya Ubangiji; zan rera yabai ga sunanka.
Por tanto yo te confesaré entre las gentes, o! Jehová, y cantaré a tu nombre.
50 Yakan ba sarkinsa nasarori; yakan nuna alheri marar ƙarewa ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.
Que engrandece las saludes de su rey, y que hace misericordia a su ungido David, y a su simiente para siempre.